Yayin da ya rage kwanaki huɗu kacal a fara Gasar Kofin Duniya ta 2026 da ƙasashen Amurka, Mexico da Canada zasu karɓi baƙunci, mahukuntan Amurka sun sanar da tawagar ƙwallon ƙafa ta Iran cewa ‘yan wasanta za su riƙa shiga ƙasar ne a ranakun wasanninsu kawai, sannan su fice bayan kammala wasannin.
Matakin ya biyo bayan ci gaba da takun-saƙa da rashin jituwar siyasa tsakanin ƙasashen Amurka da Iran. Saboda haka, tawagar Iran ta zaɓi yada zango a ƙasar Mexico duk da cewa tun farko an shirya za ta zauna a birnin Tucson da ke Jihar Arizona a Amurka.
Jakadan Iran a Mexico, Abolfazl Pasandideh, ya ce tawagar za ta shiga Amurka ne da safe a ranar wasa sannan ta bar ƙasar kafin faɗuwar rana. Ya bayyana cewa an ɗauki wannan tsari ne domin bin ƙa’idojin da aka gindaya musu.
Iran za ta buga wasanni uku na matakin rukuni a Amurka, inda za ta fafata a biranen Los Angeles da Seattle yayin gasar wadda za ta haɗa ƙasashe daga sassa daban-daban na duniya.














Discussion about this post