ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

by Abubakar Abba and Sulaiman
10 hours ago
NNPC

A makon da ya gabata, Jiragen Ruwa shida ɗauke da aƙalla Man Fetur samfarin PMS Lita miliyan da Man Dizil 212.7 da aka ƙiyasta kuɗinsu ya kai Naira biliyan 279, sun isa, Tashoshin Jiragen Ruwa na ƙasar nan.

Wannan na zuwa ne, a yayin da Matatar Mai ta Ɗangote, ke ci gaba da dakon umarnin babbar kotun tarayya kan ƙarar da mahukuntan Matatar ta shigar a gaban kotun, na a dakatar da shigo da Man Fetur da aka tace a ƙetare, zuwa cikin ƙasar nan.

Sai dai, kamfanin Man Fetur na ƙasa NNPCL da kuma ƙungiyoyin dilalan Man Fetur da ke a ƙasar, tuni, suka ƙalubalanci, wannan buƙatar, ta mahukuntan Matatar Man ta Ɗangote.

ADVERTISEMENT

Rahoton Hukumar ta NPA na shigowa da kayan cikin ƙasar nan da kuma fitar da su, ya sanar da shigo da Man na Fetur da Dizil a ranar Laraba.

Jiragen, sun sauka ne, a Tashoshin Apapa da Tincan da ke a jihar Legas da kuma ta Kalaba, inda kuma wasu Jiragen, za su gaba da sauka.

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

A cewar rahoton, Jirage shida ne, suka yi dakon  na Man Fetur, inda kuma ɗaya, ya ɗauko, Man Dizil.

Gaba ɗayan Jiragen, sun ɗauko kayan da nauyin su, ya kai daga metric tan 157,000 na Man Fetur, inda kuma na Man Dizil ya kai metric tan 132,000 tare da kuma Man AGO metric tan 25,000.

Farashin Man a yanzu a Matatar Man Ɗangote, ya kai Naira 1,250 kan kowacce Lita ɗaya, wanda aƙalla, ya kai Lita biliyan 229.1.

Kazalika, Man Dizil, ya kai Lita miliyan 29.4, wanda duk farashin Lita ɗaya, ya kai Naira 1,700 a Matatar ta Ɗangote.

Duba da hauhawan farashin kuɗaɗen musaya na ƙasashen waje, musamman na dala wanda Naira ta kai kan farashin 1,360 kan kowacce dala ɗaya, hakan ya nuna cewa, jimlar kuɗin kayan da aka shigo da su, sun kai kimanin dala miliyan 205.

Ta shigar da Aaknata Janar na ƙasa Lateef Fagbemi SAN da kuma kamfanin Man Fetur na ƙasa, NNPCL a gaban babbar kotun tarayya da ke a jihar Legas.

Kmafanin, ya buƙaci kotun da ta dakatar da hukumar haƙo Mai na cikin Ruwa, da ci gaba da bai wa, dilalan Man Fetur a cikin ƙasar nan Lasisin, damar  shigo da Man, wanda Matatar ta  Ɗangote, ta yi iƙirarin cewa, hakan na ci gaba da yin zagon ƙasa, kan ƙoƙarin da ake ci gaba da yi, na tace Man da kuma zuba jari, a fannin, a cikin ƙasar.

Aliko Ɗangote dai, ya sha zargin wasu kamfanonin Mai da wasu jami’ai a fannin tace Man a ƙasar nan, kan yin zagon ƙasa, na ci gaba da shigo da Man da aka tace, daga ƙetare, zuwa cikin ƙasar nan, duk da cewa, Matatarsa, na tace Man da ya kai yawan Ganguna, 650,000 ako wacce rana.

NNPC
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
NNPC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu
  • Sulaiman
    Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai
  • Sulaiman
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

MASU ALAKA

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Next Post
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

June 20, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.