ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

by Sani Anwar
7 months ago
Amurka

Kafin Nijeriya ta samu cikakken zaman lafiya da tsaro a fadin Arewa da kuma kudancin kasar, dole ne kowa da kowa ya ba da tasa gudunwara.

Wannan ne ra’ayin mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III da kuma tsohon Shugaban Hafsan Sojoji, Abubakar Danbazau, sun bayyana wannan ra’ayi nasu ne a ranar Litini da ta gabata, a wajen taron koli na dandalin tattaunawa da harkar tsaro, karo na farko da Gwamnatin Jihar Kebbi tare da hadin gwiwar ‘Arewa Broadcast Media Practitioners Forum’ (ABMPF), suka shirya a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Birnin Kebbi.

  • Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
  • Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sultan Sa’ad, ya bayyana taron a matsayin wanda aka shirya a daidai lokacin da ya dace, kuma ‘yan wannan kasa za su fahimci gaskiya da sanin inda aka sanya gaba, a cewarsa; al’ummar kasar nan na fuskantar hare-hare da kashe-kashe da kuma garkuwa da mutane.

ADVERTISEMENT

“Wannan wani taro ne da za a tattauna batutuwan da suka shafi rashin tsaro bayan taron da muka gudanar kwanan nan a taron masu rike da sarautun gargajiya da aka yi a Kebbi,” in ji shi.

Ya ce, za su dauki matakin kawar da duk wani nau’in ‘yan fashi da sauran miyagun ayyuka a Arewacin Najeriya.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Haka zalika, ya buga misali da Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, da aka yi garkuwa da shi, kuma aka biya wadanda suka sace shi miliyoyin kudade kafin a sako shi, wanda ya bayyana hakan a matsayin babban abin takaici.

Dangane da batun Shugaban Amurka Donald Trump, Sultan Sa’ad ya bukaci Nijeriya da kada ta bari wasu kasashe su raba kawunansu, ya kuma bayar da tabbacin cewa; duk da kalubalen da ake fuskanta, Nijeriya za ta ci gaba da kasancewa mai girma da kuma ci gaba da samun hadin kai.

Har ila yau, Tsohon Babban Hafsan Sojin Kasa, Abubakar Danbazau, a jawabinsa ya bayar da shawarar cewa; dole ne a magance matsalar rashin tsaro, matsalolin fatara, sauyin yanayi, rashin aikin yi da kuma amfani da kudaden tarayya da aka kayyade.

A cewarsa, kwararar masu tsattsauran ra’ayin addini cikin kasar, ya taimaka wajen tabarbarewar tsaro da ke bukatar daukar matakin yaki da su ko kuma korar su daga kasar baki-daya.

Kazalika, ya kuma bukaci Gwamnonin Arewa da su yi amfani da kudaden asusun tarayya, ta hanyar samar da guraben ayyukan yi da samar da karin masana’antu, domin samun ci gaban tattalin arziki.

A cewar tasa, alkaluma sun nuna cewa; sakamakon ayyukan ‘yan fashi da makami, ya hana kimanin yara miliyan 10 shiga makarantun firamare da sakandare a Arewacin Najeriya.

Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, a wani faifan bidiyo da ya gabatar a wurin taron, ya yaba wa wadanda suka shirya taron, musamman ganin cewa; an riga an tattauna batun rashin tsaro a taron Kungiyar Gwamnonin Arewa.

“An yi matukar samun nasarori a wannan taro, kana kuma an tura jami’an tsaro ko’ina a Arewacin kasar nan,” in ji shi.

 

Gwamna Uzodimma Ya Bukaci Sarakunan Gargajiya Su Jagoranci Yi Wa Kasa Adduo’I’n Zaman Lafiya

Biyo bayan matsin lamba da ake yi wa Nijeriya, kan kashe-kashen da rashin tsaro ke haifarwa, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC, Cif Hope Uzodimma, ya yi kira ga Sarakunan gargajiya da su rika yin addu’o’i, domin samun saukin matsalar tsaro.

Uzodimma, wanda shi ne Gwamnan Jihar Imo, ya jagoranci sauran gwamnonin wajen kai wa Gwamna Mohammed Umar Bago na Jihar Neja ziyara, domin jajanta masa kan asarar rayuka da dama da aka yi a Jihar, a kwanakin baya.

Gwamnan ya kara da cewa, duk da kokarin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, na karfafa tsarin tsaron kasar, ya kamata Sarakunan Gargajiya su yi amfani da nasu hanyoyin da za su kawo karshen rashin tsaro.

“Ina kira ga Sarakunan Gargajiya, da su hada kan al’ummar kasar nan, domin kare al’umma, shugaban kasa, ya himmatu wajen samar da ayyuka, kuma mu a kananan hukumomi; mun dukufa wajen aiwatar da dukkanin manufofinsa, kana kuma; nuna shugabanci na gari shi ne abin da muka sanya gaba,” in ji shi.

Dangane da dalilin ziyarar Gwamna Bago, ya ce; sun je jihar ne, domin jajanta wa gwamnati da jama’a, dangane da haduran jiragen ruwa da na tankar mai da rashin tsaro da suka yi sanadiyyar salwantar rayuka da dama tare da raba mutane da dama da gidajensu.

Ya ce, “Mun zo ne, domin mu yi wa dan’uwanmu ta’aziyya tare da karfafa masa gwiwa, mu kuma bayar da gudunmawar kudi da addu’o’i, da kuma bai wa iyalan wadanda iftila’in ya afka hakuri tare yi musu ta’aziyyar rashin da suka yi”.

“Gwamna Bago, na daya daga cikin mafi kyawun cikinmu, mafi haske, mai kuzari kuma wanda ya san makamar aiki” in ji shi.

Gwamnan Jihar Neja, Bago da Etsu Nupe da Shugaban Masu Rike da Sarautun Gargajiya na Jihar Neja, Alhaji Yahaya Abubakar, duk sun yaba da ziyarar da gwamnonin masu ci suka kawo musu jihar.

Bago ya yi tir da kalubalen tsaro da dimbin bala’o’i da suka addabi jihar, ya kuma ce; gwamnati ta dukufa wajen ganin an samu zaman lafiya.

Gwamnonin da suka ziyarci Minna, sun hada da na Jihohin Delta, Kogi, Ebonyi, Imo da kuma Legas, yayin da Mataimakan Gwamnonin Jihohin Jigawa, Kebbi da Sokoto, suka wakilci nasu gwamnonin.

Amurka
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.