A yau Juma’a ne gwamnatin Japan ta kaddamar da hukumar binciken sirri ta kasa, da nufin inganta ikon kasar na tattara bayanan sirri, matakin da ya zamo gabar kammala sake dunkule tsarin aiwatar da binciken sirri na kasar wuri guda, sabanin rababben tsarin da kasar ta kwashe sama da shekaru 80 tana aiki da shi tun bayan yakin duniya na biyu.
Rahotanni na cewa, a halin yanzu firaministar kasar ce za ta rike ragamar koli ta tsare-tsaren binciken sirri, an kuma dunkule gamayyar ikon binciken sirri na sassa daban daban na gwamnatin kasar wuri daya. Wannan zuzzurfan sauyi a tsarin binciken sirri, ba wai salo ne na kyautata aikin hukuma ba, maimakon hakan, tsarin aikin gwamnati ne da aka shirya domin gaggauta farfadowa da karfin sojin kasar ta Japan.
Kazalika, da hakan tsarin tsaron kasar zai kara dinkewa waje guda, tare da samun karsashi a fannin ayyukan soji, wanda hakan zai daga matsayin fargabar tsaro a shiyyar.
Wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, ya tattara ra’ayoyin al’ummun sassan duniya har mutum 3,028, kuma kaso 86.5% na masu bayyana ra’ayoyin na ganin wannan wani gagarumin sauyi ne da Japan ta aiwatar, a tsarin binciken sirri tun bayan yakin duniya na biyu, kana kaso 77.7% sun yi amannar cewa hakan na iya kaiwa ga amfani da karfin mulki ba bisa ka’ida ba, kuma mataki ne dake nuna rashin hangen nesa da kaucewa bin ka’ida.
Kazalika, kaso 83% sun bayyana damuwar cewa, hakan zai haifar da fito-na-fito tsakanin sassan shiyyar a fannin binciken sirri, kana zai yi matukar gurgunta yanayin tsaro mai rauni da kasashen shiyyar ke ciki.
Bugu da kari, kaso 87.6% na ganin matakin gwamnatin ta Japan, kari ne kan Japan da take aiwatarwa, na ballewa daga dabaibayin odar kasa da kasa da aka sanya mata bayan yakin duniya na biyu, da gaggawar da take yi na sake farfado da karfin sojinta. Ya wajaba al’ummun kasa da kasa su kara azamar sanya ido kan matakai masu hadari da Japan ke dauka na farfado da karfin dakarun sojin kasar. (Saminu Alhassan)














