ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bishap Kukah Ya Bayyana Dalilin Tilasta Wa Ƴan Siyasa Sa Hannu A Yarjejeniyar Zaman Lafiya

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Kukah

Shugaban Kwamitin Ƙasa na Zaman Lafiya, Matthew Hassan Kukah, ya bayyana dalilin da ya sa ake buƙatar ƴan siyasa su sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya kafin da bayan zaɓe.

Kukah, Bishof na Katolikan Sokoto Diocese, ya yi wannan jawabi ne a wajen taron masu ruwa da tsaki da gabatar da yarjejeniyar zaman lafiya da aka yi wa sharhi, wanda The Kukah Centre ta shirya tare da goyon bayan European Union a Abuja ranar Litinin.

  • Ƴansanda Sun Ƙaddamar Da “Operation Kukan Kura” A Kano, Sun Cafke Mutune 98.
  • Manyan Jami’o’in Kasar Sin Sun Samar Da Karin Guraben Karatu 38,000 Cikin Shekaru Biyu Da Suka Gabata

Ya ce yarjejeniyar zaman lafiya an tsara ta ne don ƙarfafa ƴan siyasa su kasance masu ɗabi’a, yana mai jaddada cewa da zarar an sanya hannu, nauyin kiyaye zaman lafiya ba wai kawai kan ƴan siyasa bane, har ma kan ƴan Nijeriya , kafofin yaɗa labarai, da ƙungiyoyin farar hula.

ADVERTISEMENT

“Lokacin da ƴan siyasa suka sanya hannu kan yarjejeniya, ba kawai ga kwamitin zaman lafiya bane. Yana zama nauyin kowa ya tabbatar an bi shi,” in ji Kukah.

Ya lura cewa tashin hankali na siyasa, yaɗuwar labaran ƙarya, da matsalolin tsaro suna ci gaba da barazanar sahihancin zaɓe, inda ya ƙara da cewa an kafa kwamitin don tallafa wa sulhu, gina amincewa, da kyakkyawar niyya tsakanin ƴan siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

A cewar shi, ayyukan sirrin kwamitin sun taimaka wajen samar da mafita masu amfani da rage rikice-rikice yayin gasa ta zaɓe.

Kukah ya ce dole ne zaɓe ya kasance cikin lumana, mai gaskiya, kuma abin amincewa, yana tunatar da ƴan siyasa cewa a kowane gasa, za a samu masu nasara da waɗanda ba su ci ba.

Ya buƙaci ƴan siyasa su ɗauki yarjejeniyar zaman lafiya a matsayin haƙiƙanin alƙawari ga ƴan Nijeriya, yana gargaɗin cewa doka kaɗai ba za ta iya tabbatar da zaman lafiya ba idan ba a canza hali ba.

“Doka tana da kyau, amma zuciyar ɗan’Adam ma dole ta canza. Idan mutane ba su da niyya, sai su zama tushen rikici,” in ji shi.

Kukah ya ƙara da cewa taron ya ba da dama don yin nazari kan yanayin zaɓe na yanzu da gano wuraren da kwamitin zai iya amfani da ikon darajar sa don tallafawa sahihancin zaɓe.

Har ila yau, ya yi kira ga kafafen watsa labarai, kungiyoyin farar hula, da hukumomin tsaro da su ci gaba da aiki tare don gina Nijeriya mai zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Kukah
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Next Post
Yaƙin Iran: Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Matakan Tsaro A Yankin Gabas

Ko Shirin Ciyar Da Mabuƙata Buɗa Baki Na Bilyan Ɗaya Ya Yi Tasiri A Sakkwato?

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.