ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Na Tarihi

by Isah Abdullahi
3 years ago
Fadar Zazzau

Wannan masallaci an fara samar da shi ne a matsayin masallacin Juma’a a shekara ta 1836, a wata Unguwa da ta yi shuhura kan karantar da addinin musulunci da ake kira Unguwar Jumatun kafin jihadin Shehu Usman Dan Fodiyo.

Fitaccen masanin tarihin nan kuma Sarkin Ayyukan Zazzau, Malam (Barista) Muhammad Abbas Fagachi ya yi wa wakilinmu tsakure kan tarihin wannan masallaci inda ya ce tun a shekarar da aka ambata, aka fara ginin wannan masallaci a Unguwar Juma da aka ambata a zamanin Sarkin Zazzau Malam Musa.

  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Yi Bincike Kan Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau

“Bayan jihadin Shehu Dan Fodiyo sai Malam Musa Sarkin Zazzau na wancan lokaci ya nemi izini wajen Shehu na ya dawo da masallacin Juma’a na Zazzau da ke Unguwar Juma, kamar yadda aka ambata a baya, sai Shehu Dan Fodiyo ya amince masa. Allah cikin ikonsa, Sarkin Zazzau Malam Musa bai sami damar cika burinsa na gina massalacin a Kofar Fadar Zazzau ba, sai Allah ya karbi rayuwarsa. Wanda ya zama Sarkin Zazzau bayan Malam Musa shi Malam Abdulkarimu, ya na hawa karagar Zazzau sai ya fara yunkurin aiwatar da kudurin marigayi sarkin da ya gada wato Malam Musa.”
Dangane da inda masallacin yake a yau kuwa, Malam Abbas Fagachi Sarkin Ayyukan Zazzau ya shaida wa wakilinmu cewar wasu gine -gine da sarakunan Zazzau suka yi domin aje kayayyakin tarihi da suka shafi masarautar Zazzau ne aka kwashe tare da dora harsashin ginin masallacin.

ADVERTISEMENT

“A lokacin da mai martaba Sarkin Zazzau Abdulkarimi ya yanke shawarar fara gina masallacin da Shehu Dan Fodiyo ya amince masa, kwatsam sai aka habarta masa wani fitaccen magini da ke wata Unguwa a birnin Zariya, maginin sunansa Muhammadu Durugu, nan take sarki ya sa aka kira shi, ba tare da bata lokaci ba ya fara ginin masallacin a Kofar Fadar Zazzau inda masallacin yake a yau.

“A kwai zantuka masu harshen damo da suka bayyana yadda wannan bawan Allah magini ya aiwatar da bukatar Sarkin Zazzau Malam Abdulkarimi, wato kamar yadda yawan wadanda suke jefa masa laka a lokaci guda ba tare da laka ko kuma tubali daya ya dawo kasa ba.”

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Wannan magini a wadancan shekaru, a cewar Sarkin Ayyukann Zazzau Malam Abbas Fagachi, ya na zaune ne a wannan Unguwa da a yau ake kira da Unguwar Babban Gwani. Kuma bayan kammala gina masallacin saboda gamsuwa da Sarkun Zazzau Malam Abdulkarimi ya yi na yadda wannan magini ya aiwatar da bukatar Sarki, sai aka nada shi Sarkin Maginan Zazzau, inda har zuwa yau zuriyyar Muhammadu Durugu ne ke sarautar Sarkin Magina a Zazzau.

Sarkin Ayyukan na Zazzau ya kuma shaida wa wakilinmu cewa, ko bayan Sarkin Zazzau Malam Abdulkarimi tun daga kan Sarkin Zazzau Malam Jafar Dan Isiyaku har zuwa Sarki Shehu Idris, a zamanin kowanne Sarki sai da aka yi wa wasu sassan masallacin gyare-gyare, musamman a zamanin Sarkin Muhammadu Aminu ne aka yi wa masallacin gyaran da aka sa siminti, haka nan a zamanin Sarkin Shehu Idris an yi gyare -gyare masu yawan gaske.

A lokacin da mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya hau karagar Zazzau, a cewar Sarkin Ayyukan Zazzau, ya furta yiwuwar yin gyare -gyare a wannan masallaci, domin abin da ya gani na nau’in kasar da ke masallacin. A lokacin da ya fara gyare-gyare a cikin Fadar Zazzau, ya kudiri aniyar gyara duk ginin masallaci da aka yi da kasa. Amma Allah cikin ikonsa, sai wannan matsala ta rushewar rufin masallacin ya auku, inda mutum takwas suka rasu wasu kuma da dama suka sami munanan raunuka.
Bayan faruwar wannan matsala da kwana daya mai martaba Sarkin Zazzau, ya bayar da umurnin rufe masallacin, har sai an gyara za a ci gaba da salloli a ciki.

Wani abu kuma da ganau a lokacin da matsala ruftawar ginin ta auku ya bayyana wa wakilinmu shi ne, al’amarin ya faru sarkin ya je bude masallacin Juma’a a karamar hukumar Soba, “yana dawowa sai ya ga al’umma a fadarsa, ya tambaya aka ce ga abin da ya faru, nan ta ke ya cire alkyabbarsa, har gudu ya yi zuwa cikin masallacin, da shi aka rika zakulo wadanda kasa ta rufe su, aka ciro wasu gawa, wasu kuma sun sami mummunan raunuka.

“Kuma mai martaba Sarkin Zazzau ya aika da sakon kudi ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu, domin gudanar da jana’izarsu, kuma ya nemi a kawo gawarwakin Fadar Zazzau, domin yi ma su Sallah, tun kafin fara sallah ruwan sama kamar da bakin kwarya aka yi har kammala sallar gawarwakin ana ruwa ba tare an sa wa mai martaba Sarki lema ba.

“A game da batutuwan da ake yi cewa wasu matsaloli ne suka sa masallacin ya fada wa wadanda ke sallah, duk jita-jita ne, illa kasar da aka rufe masallacin fiye da shekara dari biyu ita ce ta mutu, Allah kuma ya aiwatar da ikonsa a wannan rana da rufin ya fada wa al’umma da suke sallar la’asar.” In ji ganau din.

Fadar Zazzau
Isah Abdullahi
+ postsBio
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Mun Dauki Matakan Fito-na-fito Da Masu Kawo Gurbataccen Taki A Kasuwarmu – Masu Sayar Da Taki
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Matsalar Da Mata Ke Ciki Ta Sa Na Rungumi Rubuce-rubuce -Hajiya Hafsat Barau
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

MASU ALAKA

Fadar Zazzau
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Fadar Zazzau
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Ketare Ya Karu A Watanni 7 Na Farkon Bana

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Ketare Ya Karu A Watanni 7 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.