ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Na Tarihi

by Isah Abdullahi
3 years ago
Fadar Zazzau

Wannan masallaci an fara samar da shi ne a matsayin masallacin Juma’a a shekara ta 1836, a wata Unguwa da ta yi shuhura kan karantar da addinin musulunci da ake kira Unguwar Jumatun kafin jihadin Shehu Usman Dan Fodiyo.

Fitaccen masanin tarihin nan kuma Sarkin Ayyukan Zazzau, Malam (Barista) Muhammad Abbas Fagachi ya yi wa wakilinmu tsakure kan tarihin wannan masallaci inda ya ce tun a shekarar da aka ambata, aka fara ginin wannan masallaci a Unguwar Juma da aka ambata a zamanin Sarkin Zazzau Malam Musa.

  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Yi Bincike Kan Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau

“Bayan jihadin Shehu Dan Fodiyo sai Malam Musa Sarkin Zazzau na wancan lokaci ya nemi izini wajen Shehu na ya dawo da masallacin Juma’a na Zazzau da ke Unguwar Juma, kamar yadda aka ambata a baya, sai Shehu Dan Fodiyo ya amince masa. Allah cikin ikonsa, Sarkin Zazzau Malam Musa bai sami damar cika burinsa na gina massalacin a Kofar Fadar Zazzau ba, sai Allah ya karbi rayuwarsa. Wanda ya zama Sarkin Zazzau bayan Malam Musa shi Malam Abdulkarimu, ya na hawa karagar Zazzau sai ya fara yunkurin aiwatar da kudurin marigayi sarkin da ya gada wato Malam Musa.”
Dangane da inda masallacin yake a yau kuwa, Malam Abbas Fagachi Sarkin Ayyukan Zazzau ya shaida wa wakilinmu cewar wasu gine -gine da sarakunan Zazzau suka yi domin aje kayayyakin tarihi da suka shafi masarautar Zazzau ne aka kwashe tare da dora harsashin ginin masallacin.

ADVERTISEMENT

“A lokacin da mai martaba Sarkin Zazzau Abdulkarimi ya yanke shawarar fara gina masallacin da Shehu Dan Fodiyo ya amince masa, kwatsam sai aka habarta masa wani fitaccen magini da ke wata Unguwa a birnin Zariya, maginin sunansa Muhammadu Durugu, nan take sarki ya sa aka kira shi, ba tare da bata lokaci ba ya fara ginin masallacin a Kofar Fadar Zazzau inda masallacin yake a yau.

“A kwai zantuka masu harshen damo da suka bayyana yadda wannan bawan Allah magini ya aiwatar da bukatar Sarkin Zazzau Malam Abdulkarimi, wato kamar yadda yawan wadanda suke jefa masa laka a lokaci guda ba tare da laka ko kuma tubali daya ya dawo kasa ba.”

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Wannan magini a wadancan shekaru, a cewar Sarkin Ayyukann Zazzau Malam Abbas Fagachi, ya na zaune ne a wannan Unguwa da a yau ake kira da Unguwar Babban Gwani. Kuma bayan kammala gina masallacin saboda gamsuwa da Sarkun Zazzau Malam Abdulkarimi ya yi na yadda wannan magini ya aiwatar da bukatar Sarki, sai aka nada shi Sarkin Maginan Zazzau, inda har zuwa yau zuriyyar Muhammadu Durugu ne ke sarautar Sarkin Magina a Zazzau.

Sarkin Ayyukan na Zazzau ya kuma shaida wa wakilinmu cewa, ko bayan Sarkin Zazzau Malam Abdulkarimi tun daga kan Sarkin Zazzau Malam Jafar Dan Isiyaku har zuwa Sarki Shehu Idris, a zamanin kowanne Sarki sai da aka yi wa wasu sassan masallacin gyare-gyare, musamman a zamanin Sarkin Muhammadu Aminu ne aka yi wa masallacin gyaran da aka sa siminti, haka nan a zamanin Sarkin Shehu Idris an yi gyare -gyare masu yawan gaske.

A lokacin da mai martaba Sarkin Zazzau Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya hau karagar Zazzau, a cewar Sarkin Ayyukan Zazzau, ya furta yiwuwar yin gyare -gyare a wannan masallaci, domin abin da ya gani na nau’in kasar da ke masallacin. A lokacin da ya fara gyare-gyare a cikin Fadar Zazzau, ya kudiri aniyar gyara duk ginin masallaci da aka yi da kasa. Amma Allah cikin ikonsa, sai wannan matsala ta rushewar rufin masallacin ya auku, inda mutum takwas suka rasu wasu kuma da dama suka sami munanan raunuka.
Bayan faruwar wannan matsala da kwana daya mai martaba Sarkin Zazzau, ya bayar da umurnin rufe masallacin, har sai an gyara za a ci gaba da salloli a ciki.

Wani abu kuma da ganau a lokacin da matsala ruftawar ginin ta auku ya bayyana wa wakilinmu shi ne, al’amarin ya faru sarkin ya je bude masallacin Juma’a a karamar hukumar Soba, “yana dawowa sai ya ga al’umma a fadarsa, ya tambaya aka ce ga abin da ya faru, nan ta ke ya cire alkyabbarsa, har gudu ya yi zuwa cikin masallacin, da shi aka rika zakulo wadanda kasa ta rufe su, aka ciro wasu gawa, wasu kuma sun sami mummunan raunuka.

“Kuma mai martaba Sarkin Zazzau ya aika da sakon kudi ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu, domin gudanar da jana’izarsu, kuma ya nemi a kawo gawarwakin Fadar Zazzau, domin yi ma su Sallah, tun kafin fara sallah ruwan sama kamar da bakin kwarya aka yi har kammala sallar gawarwakin ana ruwa ba tare an sa wa mai martaba Sarki lema ba.

“A game da batutuwan da ake yi cewa wasu matsaloli ne suka sa masallacin ya fada wa wadanda ke sallah, duk jita-jita ne, illa kasar da aka rufe masallacin fiye da shekara dari biyu ita ce ta mutu, Allah kuma ya aiwatar da ikonsa a wannan rana da rufin ya fada wa al’umma da suke sallar la’asar.” In ji ganau din.

Fadar Zazzau
Isah Abdullahi
+ postsBio
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Mun Dauki Matakan Fito-na-fito Da Masu Kawo Gurbataccen Taki A Kasuwarmu – Masu Sayar Da Taki
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Buhari Ya Yi Duk Abin Da Ya Dace Wajen Magance Matsalolin Nijeriya – Shagalinku
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Matsalar Da Mata Ke Ciki Ta Sa Na Rungumi Rubuce-rubuce -Hajiya Hafsat Barau
  • Isah Abdullahi
    https://hausa.leadership.ng/author/isah-abdullahi/
    Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Ketare Ya Karu A Watanni 7 Na Farkon Bana

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Ketare Ya Karu A Watanni 7 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.