Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.
Jama’a barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, wanda yake tattaunawa game da abin da yake ci wa al’umma tuwo a kwarya.
A wannan mako zan dan kara jan hankali a kan lokutan da ya kamata mu kara kusanci ga ubangiji, mu samu lada mu ji kai. A wannan wata da yake gabato mu na Ramadan, ya kamata mu daure, mu cije wajen ayyukan alkhairi.
Allah subhanahu wata a’ala ya fifita watan Ramadana a cikin watanni da yawa, wata ne me falala da Allah yake bude kofofin rahmarsa. Amma sai a cije, masu kudi, ‘yan kasuwa sai su daura damara su kara kudin kaya.
Ba ma ga masu kudi ba, su kansu talakawa sai su hade rai, su wata ne na neman kudi, haka kawai sai an yi kudi a wannan watan, sai an takura sai an zafafa. Hatta kankara in kana siyan kankara naira dari za ta koma dari biyar har naira dubu daya, saboda kawai lokaci ne da za a yi amfani da ita.
Kwana ashirin da tara ne, amma wani shi sai ya zafafa abin da shekara guda ma bai zafafa ba. Ya ilahil’alamina lokaci ne da ya kamata mu yi amfani da shi mu samu lada, amma shi ne ya zama na tsawwalawa. Idan fa ka saukaka fa Allah zai saukaka maka.
A iya watannin nan Allah sai ya yi maka gafarar da shekara ashirin kana neman gafara bai yi maka ba, Allah sai ya yi maka arzikin da shekaru talatin kana neman arzikin bai yi maka ba, Allah sai ya yi maka budin da shekara arba’in kana nema bai yi maka ba, sai ya yi maka a wannan watan.
To, ka ga wata ne da ya kamata kai ma ka tausaya, kai ma Allah sai ya tausaya maka. Idan ka taimaki mutum daya ya ji dadi to, Allah zai yi maka budin da za ka ji dadi har abadan abidina. Dan haka ‘yan’uwa dan Allah duk abin da aka san dan’uwa musulmi ya na amfani da shi dan ya sha ruwa ya ji dadi a ransa dan Allah mu saukaka.
Na tabbatar akwai abubuwan da aka siye su da dadewa irinsu, barkono, kayan citta, kayan shayi, da su mai, akai ta bobboyewa su waken suya da waken kosai da ake yi. To, dan Allah ‘yan’uwa mu duba girman musulinci mu duba girman watan, mu duba ‘yan’uwantaka da zumuntaka, dan Allah kar mu zafafa, mu saukaka kayan amfani yadda kowa zai iya amfana. Hatta kankana sai ka ji ana dubu biyar, a yanzu dai kana iya siyen dubu daya, dari biyar, amma a wannan wata har dubu biyar, sai ka ce ta gwal.
To, dan Allah ‘yan’uwa musulmi ina mai bamu shawara, lokaci ne da za mu samu dama da za mu samu kusanci ga ubangiji. Abin da muka dade muna roko sai ka ga Allah ya ba mu saboda tausayawa da muka yi. Wanda kuma Allah ya basu iko da tausayawa na taimakawa marayu da makofta, akwai wadanda suna cikin wani hali, wani yakan adana abin da zai adana tun daga daya ga watan ramadan har izuwa ranar sallah.
Wani kuma kullum sai ya fita zai samu abin da ma zai kawo wa iyalinsa a ci, idan Allah ya sa kana da wannan damar to, ka taimaka, kai ma sai Allah ya baka, ka kuma tausaya. Ga marayu nan wasu sai sun yi bara za su samu, to irin wannan damar da ka samu Allah ya bude maka kofofi to, kai ma sai ka samar domin Allah ya tausaye ka.
Allah ya sa mu dace, ubangiji Allah ya sa mu shiga wannan watan cikin nasara da albarka, Allah ya sa albarka a cikin rayuwarmu baki daya.















Discussion about this post