• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Noma Za Ta Samar Da Ingantaccen Irin Farin Wake 

by Abubakar Abba
1 year ago
in Noma Da Kiwo
0
Cibiyar Noma Za Ta Samar Da Ingantaccen Irin Farin Wake 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar kula da harkokin noma ta kasa da kasa (IITA), ta shirya taron bita na kwana biyu; domin sama wa kanannan manoman kasar nan ingantacen Iri na Farin Wake.

Wani kwararre a fannin samar da Irin noma a cibiyar ta IITA, Farfesa Lucky Omoigui ya bayyana cewa, an shirya taron ne don kokarin hada masu ruwa da tsaki a wannan fanni na samar da Irin, domin samun damar tattaunawa kan aikin noma na shekarar 2024 a fadin kasar nan.

  • Sanata Yari Ya Samar Da Taki Ga Manoman Zamfara A Kan Naira 20,000
  • Hare-haren Ƴan Bindiga A Jihar Neja Sun Tilasta Wa Manoma Tserewa

Farfesan ya kara da cewa, matsalar da ake samu wajen noma wannan Farin Wake na afkuwa ne sakamakon rashin samun ingantaccen Irin noma.

Ya ci gaba da cewa, a duk shekara a Nijeriya; ana noma Farin Wake kimanin tan miliyan 2.3, duk kuwa da cewa kasar na bukatar wannan Farin Wake sama da tan miliyan 3.

A cewar Lucky, wannan matsala ta rashin samar da isasshen ingantaccen Irin Farin Waken ne ta sa ake shigo da shi daga makwabta kasashen wannan kasa, domin cike gibin da ake da shi.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Ya bayanna cewa, “Ko shakka babu, samar da wannan ingantaccen Irin Farin Wake, zai ba da damar kara yawan nomansa a fadin kasar nan, wanda kuma hakan zai kara samar da dimbin kudaden shiga ga masu nomansa tare da rage yadda ake kashe kudaden”.

Haka zalika, shugaban sashen cibiyar da ke gudanar da aikin cibiyar a Jihar Kano, Dakta Alpha Yaya Kamara a nasa jawabin a wajen taron cewa ya yi, akwai bukatar samar wa da manoma, musamman kananan da ke karkara; ingantaccen Irin Farin Wake.

Shi ma a nasa jawabin a wajen taron, shugaban kungiyar masu hada-hadar Irin noma ta kasa, Yusuf Ado Kibiya (SEEDAN) ya bayyana cewa; kungiyar ta yi hadaka da sauran cibiyoyi domin samar da ingantaccen Irin Farin Wake a fadin wannan kasa.

Ya kara da cewa, a shirye kungiyar take; don yin hadaka da sauran masu ruwa da tsaki, domin samar da ingantaccen Irin wannan Iri na Farin Wake.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BeansKiwoNomaWake
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihohi Goma Mafi Arahar Abinci A Nijeriya

Next Post

Arafat: NAHCON Ta Jagoranci Yi Wa Kasa Addu’a

Related

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

4 days ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

4 days ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

2 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

2 weeks ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

3 weeks ago
Next Post
Arafat: NAHCON Ta Jagoranci Yi Wa Kasa Addu’a

Arafat: NAHCON Ta Jagoranci Yi Wa Kasa Addu'a

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.