Jigo a jam’iyyar NDC, kuma jagoran Kwankwasiyya, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, ya nuna yiwuwar haɗa tikitin takara da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, a babban zaɓen shekarar 2027.
Kwankwaso ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi yayin wata hira kai tsaye da aka yi da shi a gidan talabijin na Trust TV.
Ya ce manufofin magoya bayan Obi, da aka fi sani da ‘Obidients’, da kuma tafiyar Kwankwasiyya suna da kamanceceniya, wanda hakan ya sa ake ƙoƙarin haɗa kai.
Da aka tambaye shi ko ‘yan Nijeriya za su iya sa ran tikitin haɗin gwiwa tsakanin Obi da Kwankwaso a ƙarƙashin NDC a 2027, tsohon ɗan takarar shugaban kasar a jam’iyyar NNPP ya ce:“Na yarda haka ne, kuma idan aka duba jam’iyyar, ina ganin haka ne tunaninsu.
“A kwanakin baya mun yi ƙoƙarin fahimtar abin da Obidients ke son yi a siyasa da kuma abin da suke son yi wa Nijeriya.
“Lokacin da muka kwatanta tafiyar su da ta mu, sai muka fahimci cewa manufofin kusan iri ɗaya ne.
“A taƙaice, muna son mu mayar da Nijeriya wuri mafi alheri ga kowa, musamman matasa maza da mata da suke buƙatar kulawar gwamnati. Ba sa buƙatar abubuwa masu yawa, sai dai muhimman abubuwa kamar ilimi, aikin yi, tsaro da makamantansu.
“Waɗannan su ne matsalolin da ake fuskanta yanzu, kuma mun yarda cewa ƙwararru za su duba tsarinmu da nasu tsarin domin kwatantawa.
“Mun yi nisa sosai a tattaunawar, kuma bisa ga abin da muka tattauna da su, na yi imani muna da buri guda ɗaya ne — ganin Nijeriya ta zama ƙasa mafi alheri ga kowa,” in ji shi.















Discussion about this post