Da safiyar yau Talata 8 ga wata ne mataimakin shugaban kasar Sin...
Read moreDetailsShugaban kasar Sin Xi Jinping, ya zanta ta wayar tarho da firaministan...
Read moreDetailsA gun taron manema labaru da ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar...
Read moreDetailsA yau Litinin ne mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar...
Read moreDetailsA ranar 7 ga watan Satumba mai magana da yawun ma’aikatar harkokin...
Read moreDetailsA makon da ya gabata ne hukumar kula da makamashi ta kasar Sin ta ce zuwa karshen watan Yulin bana, karfin tashoshin samar da lantarki daga hasken rana na kasar ya kai kilowatts biliyan 1.286, wanda a karon farko ya zarce na kwal. Wannan ya sa hasken rana ya zama hanya mafi girma ta samar da lantarki a kasar Sin. Kuma Lantarkin da aka samar daga hasken rana, ya dauki kaso 31.5 na yawan lantarkin da Sin take samarwa. Hakika kasar Sin ta mayar da makamashin hasken rana da ake ganin mai sarkakiya ne zuwa kashin bayan tsarin samar da makamashi a kasar, haka kuma makamashin da ake iya dogaro da shi. Har kullum kasar Sin na kara nuna wa duniya sabbin dabaru da manufofi da kwarewa, dake kara bayyana cewa, babu abun da ba zai yuwu ba, idan har aka jajirce aka samar da kyakkyawan tsari. Wannan ya alamta wata gagarumar nasara da Sin ta samu a kokarin da take yi na sauyawa zuwa amfani da makamashi mai tsafta da kuma rage fitar da hayakin Carbon mai gurbata muhalli. Bugu da kari, gagarumar nasara ce a shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15. Mummunan tasirin sauyin yanayi abu ne da ba ya bambance tsakanin kasashe ko al’ummomi, lamarin da ya sa shi zama wani batu mai muhimmanci da ya shafi daukacin mutanen duniya. Kasar Sin ta dauki batun tunkarar sauyin yanayi da muhimmanci. Don haka ta kowacce fuska tana iyakacin kokarin ganin ta lalubo hanyoyin da za ta rage fitar da hayaki mai guba domin bayar da gudunmawa ga kare muhalli da halittu da samar da duniya mai tsafta. Tabbas wannan nasara ba ita Sin ba ce kadai, ta duk duniya ce domin za ta kara ba kasashe kwarin gwiwar yin abun da ya kamata na ganin sun samar wa al’ummominsu makamashi mai tsafta da za a iya dogaro da shi, wanda kuma zai bayar da gudunmawa ga kokarin da ake yi na yaki da sauyin yanayi. Hakika ci gaban Sin a wannan bangare, yana nufin kasashe za su kara samun alfanu, domin zuwa yanzu, fasahar kasar Sin a wannan bangare na zama daya daga cikin wadanda ke kan gaba a duniya, inda zuwa yanzu ake gaggauta nazari da samar da ingantattun fasahohin samar da lantarki daga hasken rana da za a fara amfani da su a nan gaba. (Fa’iza Mustapha)
Read moreDetailsAn watsa shiri na farko na gasar wake-wake ta kasa da kasa...
Read moreDetailsZa a gudanar da taron tattaunawa kan zuba jari da kasuwanci na...
Read moreDetailsAn yi taron kara wa juna sani na kasa da kasa kan tunanin Xi Jinping a fannin al’adu karo na biyu jiya Lahadi 6 ga watan nan a birnin Shenzhen na lardin Guangdong da ke kudancin kasar Sin. Taron mai taken “inganta jigon al’adu don zamanantar da kasar Sin”, ya samu halartar wasu kwararru da masana gami da wakilai kimanin 130, daga cibiyoyin nazari da jami’o’in kasar Sin gami da cibiyoyin nazarin tunanin Xi Jinping a fannin al’adu da wayar da kan al’ummar kasar Sin na kasasehn waje. Mataimakin shugaban sashen yayyata ayyukan kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, Hong Dayong, ya gabatar da jawabi a gun bikin kaddamar da taron, inda ya ce, inganta ginshikin al’adu na bukatar zurfafa karatu gami da kara fahimtar tunanin shugaba Xi Jinping a fannin al’adu, da tsayawa ga ayyukan yin kirkire-kirkiren al’adu, gami da karfafa mu’amala da koyi da juna a fannin wayar da kan al’umma, yayin da ake ci gaba da nazari da kuma gadon tarihi da al’adun al’ummar kasar Sin. (Murtala Zhang)
Read moreDetailsA yau Litinin ne firaministan kasar Sin Li Qiang, ya gana da...
Read moreDetails© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.
© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.