ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Yankin Gulf Zuwa Afirka, Me Sansanonin Sojan Amurka Suka Haifar?

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Gulf

Sama da kwanaki 20 ke nan da Amurka da Isra’ila suke daukar matakan soja a kan Iran, sai dai martanin da Iran ta mayar ya sa wutar yaki har ta kama kusan dukkanin sassan yankin Gulf, lamarin da kuma ya tono mana gaskiyar yadda Amurka ke fakewa da batun kiyaye tsaro wajen kafa sansanonin sojanta a sassan duniya, duba da cewa sansanonin soja da ta kafa a kasashen yankin Gulf a maimakon su ba da kariya ga kasashen, sai ga shi har sun janyo musu hare-hare. Abin da kuma ya aza musu tambaya, wato ya kamata a dogara ga kasar da ke nuna fin karfi don ta samar musu abu na wai tsaro, ko kuma ya kamata su kiyaye mulkin kansu da kuma ’yancinsu?

 

Bisa ga kididdigar da aka yi, yanzu haka Amurka ta kafa sansanonin soja kimanin 800 a kasashe da shiyyoyi kimanin 80, sansanonin da suka taka muhimmiyar rawa a yake-yaken da Amurka ta yi cikin shekaru sama da 100 da suka wuce, wadanda kuma suka kasance muhimmiyar madogara a gare ta wajen nuna karfi da kafa babakere a fadin duniya. Amurka ta kan cimma burinta na kafa sansanoninta a wasu kasashe, ta hanyar daddale yarjejeniya da su game da samar musu tsaro, ta yadda za ta kai ga sa hannu, da ma ba da jagoranci a harkokin shiyyar. A hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kaddamar a kan Iran a wannan karo, sansanin sojan sama na Al Udeid da ke Qatar, da kuma sansanin rundunar sojan ruwa ta biyar ta Amurka da ke kasar Bahrain, duk sun zama ginshikin Amurka wajen daukar matakan soja. Daidai kamar yadda David Vine, mashahurin masanin ilmin aikin soja na kasar Amurka ya fada, cewa sansanonin soja na Amurka da ke ketare suna samar mata sauki wajen aiwatar da ayyukan soja, wadanda suka zama mafarin yake-yaken da take yi a sassan duniya.

ADVERTISEMENT

 

Sai dai ko da gaske ne sansanonin suna samar da tsaro ga kasashen da suka karbe su? Idan mun yi nazari a kan rikicin da ya faru a wannan karo, za mu gano cewa, ban da kasar Isra’ila, Iran ta kuma kai hare-hare sansanonin sojan Amurka da ke kasashen Qatar, da Kuwait, da hadaddiyar daular Larabawa, da Bahrain, da Saudiyya, da Iraki, da Jordan, kuma a cewar Iran, ba wai kasashen mashigin tekun Farisa take kaiwa hare-hare ba, a’a, sansanonin sojan da Amurka ta kafa a kasashen ne take hari.

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

 

Lallai na’urorin soja da Amurka ta girke a maimakon su samar wa kasashen tsaro, ga shi sun zama abin da ke janyo musu rashin tsaro. Dalilin hakan shi ne ainihin rawar da sansanonin suke takawa, ita ce kare muhimman muradun kasar Amurka, ko ta zama hanyar shawo kan Iran, ko samun iko a kan muhimman hanyoyin ruwa, ko kuma kwace albarkatun kasa. Amma idan rikici ya tsananta, sansanonin su kan zama wurare da ake kaiwa hare-hare.

 

A nahiyar Afirka ma, Amurka ta fake da batun “yaki da ta’addanci” da na “hadin gwiwar tsaro”, wajen kafa sansanonin soja a wasu kasashen nahiyar. Sai dai sansanonin da ma sojojin da take girkewa sun kasa samar da abu da take kira wai tsaro. In mun ba da misali da Nijer, inda kasar Amurka ta fara kafa sansanonin soja a kasar tun shekarar 2013, bisa sunan wai yaki da ta’addanci da dakaru masu tsattsauran ra’ayi a yankin Sahel. Amma sama da shekaru 10 sun wuce, ayyukan ta’addanci sun dada karuwa a maimakon raguwa. A ganin kasar Nijer, hakan ya faru ne sakamakon yadda Amurka ta fake da batun yaki da ta’addanci wajen cimma muradun kanta a shiyyar, lamarin da ya sa ta kori sojojin Amurka a shekarar 2024.

 

Hakikanan abubuwan da suka faru sun yi ta shaida cewa, amincewa da kafa sansanonin sojan kasar Amurka ya gaza samar da tsaro ga kasashen da suka karbe su. Ko a yankin Gulf ko kuma a nahiyar Afirka, ba za a kai ga tabbatar da tsaro ba, har sai an tsaya an kafa ikon kai na aiwatar da harkokin diplomasiyya, da hadin gwiwa da kasashen yankin, da kuma tabbatar da tsaro na bai daya. A lokacin da laimar kariya ta rika zama abin da ke janyo rashin tsaro, to, lokaci ya yi da ya dace a sake tunani game da me ya kamata a zaba.

Gulf
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Gulf
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
APC Ta Bayyana Shirin Taron Ƙasa Don Zaɓen 2027 — Masari

APC Ta Bayyana Shirin Taron Ƙasa Don Zaɓen 2027 — Masari

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.