ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Yankin Gulf Zuwa Afirka, Me Sansanonin Sojan Amurka Suka Haifar?

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Gulf

Sama da kwanaki 20 ke nan da Amurka da Isra’ila suke daukar matakan soja a kan Iran, sai dai martanin da Iran ta mayar ya sa wutar yaki har ta kama kusan dukkanin sassan yankin Gulf, lamarin da kuma ya tono mana gaskiyar yadda Amurka ke fakewa da batun kiyaye tsaro wajen kafa sansanonin sojanta a sassan duniya, duba da cewa sansanonin soja da ta kafa a kasashen yankin Gulf a maimakon su ba da kariya ga kasashen, sai ga shi har sun janyo musu hare-hare. Abin da kuma ya aza musu tambaya, wato ya kamata a dogara ga kasar da ke nuna fin karfi don ta samar musu abu na wai tsaro, ko kuma ya kamata su kiyaye mulkin kansu da kuma ’yancinsu?

 

Bisa ga kididdigar da aka yi, yanzu haka Amurka ta kafa sansanonin soja kimanin 800 a kasashe da shiyyoyi kimanin 80, sansanonin da suka taka muhimmiyar rawa a yake-yaken da Amurka ta yi cikin shekaru sama da 100 da suka wuce, wadanda kuma suka kasance muhimmiyar madogara a gare ta wajen nuna karfi da kafa babakere a fadin duniya. Amurka ta kan cimma burinta na kafa sansanoninta a wasu kasashe, ta hanyar daddale yarjejeniya da su game da samar musu tsaro, ta yadda za ta kai ga sa hannu, da ma ba da jagoranci a harkokin shiyyar. A hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kaddamar a kan Iran a wannan karo, sansanin sojan sama na Al Udeid da ke Qatar, da kuma sansanin rundunar sojan ruwa ta biyar ta Amurka da ke kasar Bahrain, duk sun zama ginshikin Amurka wajen daukar matakan soja. Daidai kamar yadda David Vine, mashahurin masanin ilmin aikin soja na kasar Amurka ya fada, cewa sansanonin soja na Amurka da ke ketare suna samar mata sauki wajen aiwatar da ayyukan soja, wadanda suka zama mafarin yake-yaken da take yi a sassan duniya.

ADVERTISEMENT

 

Sai dai ko da gaske ne sansanonin suna samar da tsaro ga kasashen da suka karbe su? Idan mun yi nazari a kan rikicin da ya faru a wannan karo, za mu gano cewa, ban da kasar Isra’ila, Iran ta kuma kai hare-hare sansanonin sojan Amurka da ke kasashen Qatar, da Kuwait, da hadaddiyar daular Larabawa, da Bahrain, da Saudiyya, da Iraki, da Jordan, kuma a cewar Iran, ba wai kasashen mashigin tekun Farisa take kaiwa hare-hare ba, a’a, sansanonin sojan da Amurka ta kafa a kasashen ne take hari.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

 

Lallai na’urorin soja da Amurka ta girke a maimakon su samar wa kasashen tsaro, ga shi sun zama abin da ke janyo musu rashin tsaro. Dalilin hakan shi ne ainihin rawar da sansanonin suke takawa, ita ce kare muhimman muradun kasar Amurka, ko ta zama hanyar shawo kan Iran, ko samun iko a kan muhimman hanyoyin ruwa, ko kuma kwace albarkatun kasa. Amma idan rikici ya tsananta, sansanonin su kan zama wurare da ake kaiwa hare-hare.

 

A nahiyar Afirka ma, Amurka ta fake da batun “yaki da ta’addanci” da na “hadin gwiwar tsaro”, wajen kafa sansanonin soja a wasu kasashen nahiyar. Sai dai sansanonin da ma sojojin da take girkewa sun kasa samar da abu da take kira wai tsaro. In mun ba da misali da Nijer, inda kasar Amurka ta fara kafa sansanonin soja a kasar tun shekarar 2013, bisa sunan wai yaki da ta’addanci da dakaru masu tsattsauran ra’ayi a yankin Sahel. Amma sama da shekaru 10 sun wuce, ayyukan ta’addanci sun dada karuwa a maimakon raguwa. A ganin kasar Nijer, hakan ya faru ne sakamakon yadda Amurka ta fake da batun yaki da ta’addanci wajen cimma muradun kanta a shiyyar, lamarin da ya sa ta kori sojojin Amurka a shekarar 2024.

 

Hakikanan abubuwan da suka faru sun yi ta shaida cewa, amincewa da kafa sansanonin sojan kasar Amurka ya gaza samar da tsaro ga kasashen da suka karbe su. Ko a yankin Gulf ko kuma a nahiyar Afirka, ba za a kai ga tabbatar da tsaro ba, har sai an tsaya an kafa ikon kai na aiwatar da harkokin diplomasiyya, da hadin gwiwa da kasashen yankin, da kuma tabbatar da tsaro na bai daya. A lokacin da laimar kariya ta rika zama abin da ke janyo rashin tsaro, to, lokaci ya yi da ya dace a sake tunani game da me ya kamata a zaba.

Gulf
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Gulf
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Next Post
APC Ta Bayyana Shirin Taron Ƙasa Don Zaɓen 2027 — Masari

APC Ta Bayyana Shirin Taron Ƙasa Don Zaɓen 2027 — Masari

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.