Bilkisu Ibrahim Bishasha, matashiyar ƴan Film ce, a masana’antar Kannywood.
A hirarta ta da wakilinmu na Kaduna ABUBAKAR ABBA, ta yi bayani kan abinda ya ja hankalinta, ta fara yin Film, goyon bayan da samu daga gun mahifarta, mutuwar aurenta, tare da bayyana dalilinta na rashin son auren Jarumi, a masana’antar da sauransu.
Ki ɗan gaya mana taƙaitaccen tarihin ki?
An haife ni a ƙaramar hukumar Kauru a Jihar Kaduna.
Me yana ra’ayinki shiga masana’antar Kannywood?
Tun ina ƙaramar yarinya, inda da sha’awar Film, amma a lokacin mahaifinmu na raye, ba ma zai bari, mu shiga yin Film ba.
Da na yi aure, auren ya mutu, na zo na sake yin wani auren, shi ma muka rabu da mijina, sai na ci gaba da zama a gida, daga nan, sai na cewa wa mamana, ni dai da zaman nan ma, gwara in je, in shiga Film, ta ce to idan shi ne hanyar arzikin ki, Allah ya ba ni sa a ya kuma taimaka, ke dai kawai, ki tsare kanki.
Amma wasu musamman mata da ke da cewa, sha’awar shiga Film bayan sun baro gidajensu, ba su samun damar ko ganin mai shiya Film, ke ma kin fuskanci hakan kafin ki shiga?
Gaskiya ne, ana samun wannan ƙalubalen, amma ni, gaskiya ban sha wata wahala ɓa wajen shiga Film, awaki wani abokin yaya na, wanda ina zaune ya kira ni ya ce min, akwai wani sabon kamfanin yin Film da suka buɗe, na matsan ƴan wasan Film, ko zan iya shiga, na ce masa to, a lokacin ne, ma na yiwa maman mu magana, sai ta ce, ba damuwa, to daga nan ne, na fara.
Wato dama dai, an tallata maki shida masana’antar ke nan?
Ah!, to a lokacin ne, na ce masa zan yiwa maman mu magana, idan ta amince, sai ya ce, idan ta amince, in shigo garin Kaduna za mu je, a yi gwaji, to a lokacin sai mamanmu, ta amince, daga nan ne, na fara shiga harkar Film.
Wanne Film ɗin kika fara fitowa na farko?
Mun yi wani Film da yake ƙaramin kamfani ne, gaskiya, a U-Tube aka sanya kuma daga baya, abin ya zo ya shirance.
Menene sunan Film ɗin?
Wallahi na manta tunda yanzu kusan shekaru huɗu ke nan da yinsa.
Yau shekara nawa ke nan ki ka fara yin Film gadan-gadan?
Yanzu na kai shekarun huɗu ke nan, domin a waccan lokacin wata ƴar ƙaramar kyamara ce, muke yin amfani da ita a wajen yin gwajin ɗaukar Film har wasu mutane, na yi mana dariya.
Kin yi maganar aure bayan auren ya mutu, yaya maganar ƴaƴa fa?
Allah ya bani ƴaƴa biyu.
Tunda kin ce, shekara huɗu ke nan da fara sana’ar Film, yaran ba su yi wani girma ba ke nan?
Gaskiya, ba su yi wani girma ba sosai.
Shin, kina da ra’ayin yanzu idan ƴaƴanki sun girma suka nuna sha’awar shiga Film, za ki bar su su yi?
Ni ma, na taɓa tayin cewa, idan ma, ana neman yarinya ƙarama, akwai yarinyata.
Akwai zarge-zargen da wasu ke yi cewar, a Film akwai rashin talbiyya da sauransu, ke baki fuskanci hakan ba, da har ki ke son, sa ƴaƴanki a Film?
Gaskiya ni, ban fuskanci hakan ba, saboda ni, na ɗauki Film, sana’a ce, kuma idan ka riƙe ta a sana’a, za ta riƙe ka, sana’a.
Amma ba a iya haɗa mace da namji a ɗaki ɗaya?
Ba a haɗa mace da namiji a ɗaki ɗaya.
Waɗanne Fina- Finai ne, ki ka fito a cikinsu?
Akwai na Duhun Zuciya, wanda shi ne, ƴan kallo suka fara sani na, sai kuma aka dakatar da aikin, wanda mai dogon zango ne. akwai wanda na fito, a matsayin Aljana, na kuma fito a Film ɗin, matar waye da sauransu.
Duk a cikin waɗannan Fina- Finan da ki ka zayyano, wannene tun lokacin da ku ke ɗauka, ki ka ji ya fi ba ki sha’awa?
Gaskiya, Film ɗin Halimatu ya fi bani sha’awa tun a lokacin da ake kan ɗaukarsa.
Daga shi fa sai wanne?
Duhun Zuciya shi ma ya birge ni, ni kankin kai na.
Me ya sa a zahiri, ki ke ƙaunar Film ɗin Duhun Zuciya?
Saboda labari ne, mai ɗauke da darasi, da ke koyar da bin maganar iyaye, rashin yin hakan, mutum zai yi danasani.
Su waye Jarumansa?
Ni ce, na fito mai suna Humairah kuma ni ce, na ja shirin Film ɗin, sai shi saurayi na a Film ɗin, Sabi’u.
Wacce rawa ki ka taka a Film ɗin Halimatu?
N fito ne a matsayin Amaryar Baba Ɗan Audu.
Amma Baba Ɗan Audu a cikin labarina aka fi sanin wannan sunan?
A toh! kusan dai sunan da aka sanyawa angina nawa a Film ɗin ke nan, kuma sunan gabi shi, kowa Baba Ɗan Audu.
Wato kin fito a matsayin matar Rabi’u Rikadawa a Film ɗin na Halimatu?
Na fito ne a matsayin matarsa, kuma shi ne Film ɗin da aka fi sani na sosai.
Shi me Film ɗin Halimatu ya ƙunsa ne?
Yarinya ce kamar suke zaune a cikin jin faɗin rayuwa ita da mahaifiyarta da ƴaruwarta, kafin nan, wata rana, Hajiya ta yi tafiya, sai ta ga wata yarinya a bakin Titi wasu maza da mata sun rufe ta duka, sai Habitat ta tsaya ta raba, ta ce, bari ta ɗauke ta, ta kaita gidanta, amma shi Alhajin mijin Hajiyar bai so hakan ba, to dai, ta yi masa bayani cewa, da na kowa ne, sai ya yarda.
A kwana a tashi, sai yarinyar, ta fara yin kisisina irin ta mu ta mata domin ta ja ra’ayin Alhajin.
A masana’nar wasu Jarumai ta na da masoyi wanda har soyayyar kan rikiɗewa zuwa yin aure, ko akwai wani Jarumin da a masana’antar, da ya nuna sha’awar auren ki?
Gaskiya akwai wani wanda mun shirya yin aure sai Allah ya yi masa rasuwa.
Amma ke a kan kanki, kina da sha’awar ki auri ɗan Film?
Gaskiya ni, ba zan iya aurar ɗan Film ba, saboda ina da kishi domin a wani lokacin, ina ɗewa wasu jaruman maza cewa, wallahi matan na haƙuri da ku, amma sai dai su yi dariya su ce, ai Film, ya zamar masu hanya ce ta cin abinci.
Akwai wani abu da ake cewa, jarumai maza a masana’antar Tuwo a Ƙwarya, sai ki ga sun dade, a masana’antar ba su yi kuɗi ba, amma sai wata jarumar da ta shigo harkar ta riga su yin kuɗi a masana’antar, shin me ke kawo hakan?
Ah toh! abinda ke kawo hakan, ka ga ita macen da ke a masana’antar, za ta yi samari ya na ba ta kuɗi ko jari domin kar ta dogara a harkar Film kawai, ta kan ɗan fara juya kuɗin a sana’ar da ta fara ko kuma saurayin, ya ɗan says mata motar hawa.
To amma bayan Film ke ma kina yin wata sana’ar?
Ina yin sana’ar sayar da Takalma ko Jakankunan hannu na mata
Mun gode
Nima na gode













