Wayar da kai kan dabarun yin girke-giren abinci na gargajiya da aka shirya wa mata Musulmai da kuma mabiya addinin Kirista a yankin Kasuwar Magani a karamar hukumar Kajuru a Jihar Kaduna, ya kara karafafa alaka a tsakaninsu.
Wadanda aka wayarwa da kansu guda 120, an wayar masu da kan ne a karkashin shirin kare ‘yancin Bil’adama da tabbatar da ‘yancin yin addinai.
A yayin wayar da kan, wasu matan sun girka nau’ukan abincin gargajiya daban-daban da suka hada da miyan kuka da danwake da sauransu.
Matan masu shekaru daga 19 zuwa 24, an zabo su ne daga yankuna daban-daban a karamar hukumar Kajuru.
Manufar shi ne, domin a kara wanzar da zaman lafiya da karfafa fahimtar juna a tsakaninsu biyo bayan rikice- rikicen addini da na kabilanci da suka fru a yanki a shekarun baya.
Jagoran tawagar wayar da kan, Fasto Jonathan Peter da ke a Kasuwan Magani ya ce, an shiya wayar da kan ne domin a kara karfafa dankon zumunci a tsakanin matan.
Yayin wayar da kan, matan sun fahimci muhimmancin ci gaba da zama da juna da kuma kara kaunar juna wanda hakan ya kara kawar da duk wata rashin yarda a tsaskaninsu.
Kazalika, matan sun kuma bukaci da a samar da wani bagire, musammman domin a rinka tattaunawa tare, wanda suke da yakinin hakan zai kara taimaka wa a bangaren ci gaba da zamantakewa da bai wa matan yankin kariya.
An kuma tattaunawa kan lamarin barazanar gurbatar muhalli, inda kuma aka bukaci da a gano dalilan da ke haifar da gurbatar muhali, domin a magance kalubalen baki daya.
Sun yi nuni da cewa, addinin Kirista da Musulunci sun jaddda muhimmancin kare muhalli, domin a kare lafiyar al’umma.














