Sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ne kadai zai raba gardama a zaben 2027, amma kuma jam’iyyar ce za ta iya yanke hukunci kan wa ye zai zama dan takara.
A yayin da yake magana kan jerin martanin da suka biyo bayan maganganun tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, wanda shi ne sahu na gaba wajen neman tikitin takarar jam’iyyar, cewa wannan yunkurin na yanzu zai kasance na karshe.
An fassara sharhin cewa Atiku yana nufin zai fafata takara da sauran ‘yan takarar shugaban kasa kamar Peter Obi, Rotimi Amaechi da Rabiu Musa Kwankwaso.
Abdullahi ya ce jam’iyyar ita ce mafi girma kuma tana da iko na karsheakan yadda za ta fito da dan takararta na shugaban kasa.
Wasu goyon bayan ‘yan takarar shugaban kasa a jam’iyyar ADC, sun riga sun fara jayayya kan wanda ya kamata ya dauki tutar takarar jam’iyyar a 2027.
Daya daga cikin shugabannin jam’iyya, Dele Momodu, ya ce tikitin Atiku/Obi zai kasance mafi kyau ga jam’iyya da Nijeriya.
Da yake jawaba a cikin shirin talabijin, shugaban kugiyar ‘Obedient Mobement’, Dakta Tanko Yunusa, ya jadaddada cewa mayar da tikitin takarar shuagaban kasa zuwa kudu shi ne kawai hanyar samun nasara a zaben da za su kori APC.
Ya ce tarbar girmamawa ga Obi da Kwankwaso daga wakilai a babban taron jam’iyyar na kasa ya nuna cewa suna da magoya baya masu dimbin yawa masu son su ga sun samu tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar.
“Lokacin da ya Obi zo jiharmu ta Kano, za a iya ganin hadin kai tsakaninsa da Rabiu Musa Kwankwaso. Tarbar ta kasance babba sosai, mun sha wuya kafin muka iya kula da taron jama’a. Ana ihu cewa sai Obi da Kwankwaso! Obi da Kwankwaso!” in ji shi.
Yayin da yake martani kan wannan lamari, Malam Abdullahi ya shaida cewa, “Masu goyon baya suna bayyana ra’ayinsu ne kawai, wanda abu ne na al’ada. Ba za su iya yanke hukunci ga jam’iyya ba. Suna bayyana ra’ayinsu da kuma burinsu ne kawai, wannan shi ne abin da suka yi.”















Discussion about this post