ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bayyana Dalilansa Na Yin Garanbawul A Majalisar Kasa

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago

Shawarar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na cire ministan kudi, Wale Edun, da ministan gidaje, Arc. Ahmed Musa Dangiwa, daga mukamansu ta haifar da muhawara mai zafi a fadin Nijeriya, musamman a fannin siyasa, tattalin arziki da kasuwanci.

An bayyana sauyin ne a matsayin wani karamin garambawul a majalisar ministoci, kamar yadda wata sanarwa daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya ta tabbatar.

A maimakon Wale Edun, shugaban kasa ya nada Farfesa Taiwo Oyedele, wanda aka ce an dauke shi ne domin ya jagoranci sabon salo a harkokin kudi na kasa.

ADVERTISEMENT

Wasu masu sharhi sun ce wannan sauyi bai zo da mamaki ba, duk da cewa lokacin da aka yi shi ya ba mutane mamaki. Rahotanni daga majiyoyi na cikin gwamnati sun nuna cewa cire Edun ya samo asali ne daga matsalolin lafiya.

An bayyana cewa Edun, wanda ya kai kimanin shekaru 70, ya taba yin murabus a baya a gwamnatin Jihar Lagos saboda matsalar lafiya, sannan a shekarar 2025 ma ya taba yin jinya a kasashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

A bangaren Dangiwa kuwa, majiyoyi sun ce cire shi ya samo asali ne daga rashin gamsuwar shugaban kasa da yadda yake tafiyar da aikin ma’aikatar gidaje, inda ake bukatar saurin aiwatar da ayyuka a fadin kasa.

Bayan saukarsa, Wale Edun ya nuna godiya ga shugaban kasa, yana mai cewa ya yi alfahari da damar da aka ba shi na yi wa Nijeriya hidima.

Ya ce ya fara aiki ne a matsayin shugaban kwamitin mika mulki, sannan mai ba shugaban kasa shawara kan manufofin kudi, kafin daga bisani ya zama ministan kudi.

Edun ya ce gwamnatin Tinubu ta gaji tattalin arziki mai rauni, amma sun yi kokarin daidaita shi, inda ya ce hakan ya taimaka wajen habakar tattalin arziki daga kusan kashi 2 zuwa sama da kashi 4.

Ya kuma ce an samu raguwar hauhawar farashi daga kashi 35 zuwa kusan kashi 15, yana mai cewa wadannan gyare-gyare sun taimaka wajen dawo da kwarin gwiwar masu zuba jari da kuma inganta tattalin arziki gaba daya.

A karshe, ya gode wa ‘yan majalisar zartarwa, gwamnonin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki bisa hadin kai da suka ba shi goyon baya a lokacin mulkinsa.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

MASU ALAKA

Labarai

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Labarai

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Ra'ayi Riga

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Wadagni Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyar Benin

Xi Jinping Ya Taya Wadagni Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyar Benin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.