ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bayyana Dalilansa Na Yin Garanbawul A Majalisar Kasa

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

Shawarar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na cire ministan kudi, Wale Edun, da ministan gidaje, Arc. Ahmed Musa Dangiwa, daga mukamansu ta haifar da muhawara mai zafi a fadin Nijeriya, musamman a fannin siyasa, tattalin arziki da kasuwanci.

An bayyana sauyin ne a matsayin wani karamin garambawul a majalisar ministoci, kamar yadda wata sanarwa daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya ta tabbatar.

A maimakon Wale Edun, shugaban kasa ya nada Farfesa Taiwo Oyedele, wanda aka ce an dauke shi ne domin ya jagoranci sabon salo a harkokin kudi na kasa.

ADVERTISEMENT

Wasu masu sharhi sun ce wannan sauyi bai zo da mamaki ba, duk da cewa lokacin da aka yi shi ya ba mutane mamaki. Rahotanni daga majiyoyi na cikin gwamnati sun nuna cewa cire Edun ya samo asali ne daga matsalolin lafiya.

An bayyana cewa Edun, wanda ya kai kimanin shekaru 70, ya taba yin murabus a baya a gwamnatin Jihar Lagos saboda matsalar lafiya, sannan a shekarar 2025 ma ya taba yin jinya a kasashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

A bangaren Dangiwa kuwa, majiyoyi sun ce cire shi ya samo asali ne daga rashin gamsuwar shugaban kasa da yadda yake tafiyar da aikin ma’aikatar gidaje, inda ake bukatar saurin aiwatar da ayyuka a fadin kasa.

Bayan saukarsa, Wale Edun ya nuna godiya ga shugaban kasa, yana mai cewa ya yi alfahari da damar da aka ba shi na yi wa Nijeriya hidima.

Ya ce ya fara aiki ne a matsayin shugaban kwamitin mika mulki, sannan mai ba shugaban kasa shawara kan manufofin kudi, kafin daga bisani ya zama ministan kudi.

Edun ya ce gwamnatin Tinubu ta gaji tattalin arziki mai rauni, amma sun yi kokarin daidaita shi, inda ya ce hakan ya taimaka wajen habakar tattalin arziki daga kusan kashi 2 zuwa sama da kashi 4.

Ya kuma ce an samu raguwar hauhawar farashi daga kashi 35 zuwa kusan kashi 15, yana mai cewa wadannan gyare-gyare sun taimaka wajen dawo da kwarin gwiwar masu zuba jari da kuma inganta tattalin arziki gaba daya.

A karshe, ya gode wa ‘yan majalisar zartarwa, gwamnonin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki bisa hadin kai da suka ba shi goyon baya a lokacin mulkinsa.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Labarai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
'yansanda
Labarai

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Wadagni Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyar Benin

Xi Jinping Ya Taya Wadagni Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyar Benin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.