ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan Bauchi Na APC Ya Bai Wa Daliban Jinya 201 Tallafin Karatu

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
4 years ago
APC

Dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2023 na jam’iyyar APC, Air Marshal Sadique Baba Abubakar (Mai ritaya) ya bai wa dalibai dari biyu da daya (201) tallafin karatu a bangaron kwasa-kwasan kiwon lafiya daban-daban a kwalejin koyon jinya ta Malikiyya da ke Bauchi.

Da ya ke jawabi yayin miki shaidar tallafin ga daliban da suka ci gajiyar, Sadique Baba Abubakar ya bayyana cewar kiwon lafiya sashi ne da ke da matukar muhimmanci ga al’umma, don haka ba za su yi sako-sako da harkar da ta shafi lafiya ba.

  • Gwamnan Bauchi Ya Mika Wa Sarkin Katagum Sandar Girma

Dan takarar ya jinjina tare da yaba wa kokarin Dan-Malikin Bauchi, Alhaji Aminu Muhammad bisa samar da makarantar koyon jinya mai zaman kanta a jihar da ke maida hankali wajen koyar da dalibai ilimin kiwon lafiya daban-daban.

ADVERTISEMENT

Ya kuma nuna gamsuwarsa bisa yadda tsarin zubin makatatar yake tare da nuna cewa akwai bukatar a karfafi mutanen da ke kawo irin wannan cigaban a jihar ta Bauchi.

APC

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

“Abun takaici ne a ce an fara tunanin kafa wannan makararta ne da cewa za a yi hadin guiwa da Gwamnatin jiya amma daga karshe Gwamnatin ta zame ta bar Dan Maliki shi kadai.

“To alhamdullahi wannan abun da Dan-Malikin Bauchi ya ke yi ya sanya asasin gina al’umma ne.”

Ya ce, ilimin da daliban ke samu ba kawai ma zallar taimaka musu yake ba, yana kuma taimaka wa hukumomi wajen tabbatar da kiwon al’umma.

Ya bada tabbacin cewa za su ci gaba da taimaka wa mamallakin makarantar domin kyautata koyo da koyarwa a bangaren kiwon lafiya. Ya ce, babu wani abun da ya fi lafiyan jama’a, don haka ya ce duk abun da aka zuba a bangaren lafiya ba asara aka yi ba.

Ya jawo hankalin daliban da suka ci gajiyar tallafin ilimin da su maida hankali su koyi ilimin da ya dace domin cimma manufofin da aka sanya a gaba.

Ya kuma daura da cewa za su yi zama na musamman da mai makarantar domin ganin hanyoyin da za su bi wajen ingantawa da bunkasa makarantar domin cigaban dalibai, jama’a da kuma inganta sashin kiwon lafiya a jihar.

Tun da farko da ya ke jawabin maraba, Mai mallakin kwalejin, Alhaji Aminu Muhammad ya ce an kafa kwalejin Malikiyya ne da zimmar shawo kan gibin da ake da shi na karancin jami’an kiwon lafiya a asibitin da ke jihar.

APC

Ya ce, su na koyar da kwasa-kwasai da sama a bangaren kiwon lafiya, kuma zuwa yanzu makarantar tana da dalibai sama da 3,000.

A cewarsa kwalejin tana da lasisi da amincewar hukumomin da ke kula da sashin gami da fatan cewa nan gaba za su cimma muhimman nasarori.

APC
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Zamu Iya Raba Gari Da Ronaldo Kan Tattaunawarsa Da ‘Yan Jarida – Man UTD

Zamu Iya Raba Gari Da Ronaldo Kan Tattaunawarsa Da 'Yan Jarida - Man UTD

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.