ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan Bauchi Na APC Ya Bai Wa Daliban Jinya 201 Tallafin Karatu

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
4 years ago
APC

Dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a zaben 2023 na jam’iyyar APC, Air Marshal Sadique Baba Abubakar (Mai ritaya) ya bai wa dalibai dari biyu da daya (201) tallafin karatu a bangaron kwasa-kwasan kiwon lafiya daban-daban a kwalejin koyon jinya ta Malikiyya da ke Bauchi.

Da ya ke jawabi yayin miki shaidar tallafin ga daliban da suka ci gajiyar, Sadique Baba Abubakar ya bayyana cewar kiwon lafiya sashi ne da ke da matukar muhimmanci ga al’umma, don haka ba za su yi sako-sako da harkar da ta shafi lafiya ba.

  • Gwamnan Bauchi Ya Mika Wa Sarkin Katagum Sandar Girma

Dan takarar ya jinjina tare da yaba wa kokarin Dan-Malikin Bauchi, Alhaji Aminu Muhammad bisa samar da makarantar koyon jinya mai zaman kanta a jihar da ke maida hankali wajen koyar da dalibai ilimin kiwon lafiya daban-daban.

ADVERTISEMENT

Ya kuma nuna gamsuwarsa bisa yadda tsarin zubin makatatar yake tare da nuna cewa akwai bukatar a karfafi mutanen da ke kawo irin wannan cigaban a jihar ta Bauchi.

APC

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

“Abun takaici ne a ce an fara tunanin kafa wannan makararta ne da cewa za a yi hadin guiwa da Gwamnatin jiya amma daga karshe Gwamnatin ta zame ta bar Dan Maliki shi kadai.

“To alhamdullahi wannan abun da Dan-Malikin Bauchi ya ke yi ya sanya asasin gina al’umma ne.”

Ya ce, ilimin da daliban ke samu ba kawai ma zallar taimaka musu yake ba, yana kuma taimaka wa hukumomi wajen tabbatar da kiwon al’umma.

Ya bada tabbacin cewa za su ci gaba da taimaka wa mamallakin makarantar domin kyautata koyo da koyarwa a bangaren kiwon lafiya. Ya ce, babu wani abun da ya fi lafiyan jama’a, don haka ya ce duk abun da aka zuba a bangaren lafiya ba asara aka yi ba.

Ya jawo hankalin daliban da suka ci gajiyar tallafin ilimin da su maida hankali su koyi ilimin da ya dace domin cimma manufofin da aka sanya a gaba.

Ya kuma daura da cewa za su yi zama na musamman da mai makarantar domin ganin hanyoyin da za su bi wajen ingantawa da bunkasa makarantar domin cigaban dalibai, jama’a da kuma inganta sashin kiwon lafiya a jihar.

Tun da farko da ya ke jawabin maraba, Mai mallakin kwalejin, Alhaji Aminu Muhammad ya ce an kafa kwalejin Malikiyya ne da zimmar shawo kan gibin da ake da shi na karancin jami’an kiwon lafiya a asibitin da ke jihar.

APC

Ya ce, su na koyar da kwasa-kwasai da sama a bangaren kiwon lafiya, kuma zuwa yanzu makarantar tana da dalibai sama da 3,000.

A cewarsa kwalejin tana da lasisi da amincewar hukumomin da ke kula da sashin gami da fatan cewa nan gaba za su cimma muhimman nasarori.

APC
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
APC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Zamu Iya Raba Gari Da Ronaldo Kan Tattaunawarsa Da ‘Yan Jarida – Man UTD

Zamu Iya Raba Gari Da Ronaldo Kan Tattaunawarsa Da 'Yan Jarida - Man UTD

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.