ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Gindaya Sharuddan Da Za Su Kai Ga Kafa Matatar Man Fetur A Kenya

by Sani Anwar
2 months ago
Dangote

Aliko Dangote na nuni da cewa, zai ci gaba da shirye-shiryen kafa babbar matatar man fetur a gabashin Afirka ne, kadai idan gwamnatocin yankin suka bullo da tsauraran matakan kare matatun mansu, maimakon tataccen man da ake shigowa da shi mai arha daga ketare.

Dangoten, zai ci gaba da tsare-tsaren kafa babbar matatar man ta Gabashin Afirka ne, idan gwamnatocinsu suka bullo da tsauraran matakan kariya a kan man nasu.

Har ila yau, yana da niyyar kafa sabuwar matatar ne, bayan katafariyar cibiyarsa ta Nijeriya, wadda a halin yanzu ita ce matatar man fetur mafi girma a duniya.

ADVERTISEMENT

Dangote ya yi gargadin cewa, idan ba a yi da gaske ba, Afirka za ta iya zama yankin da ya fi ko’ina tarin mai tare da sayar da shi da arha, tana kuma shigo da tataccen man daga ketare, masana’antunta na cikin gida kuma a lalace.

Ya ba da misali da kalubalen da matatar mai ta Nijeriya ke fuskanta, saboda rashin adalcin tsarin gyaran matatun cikin gida, wanda hakan ke barazana ga zuba jari.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

Shugaban Faransa Emmanuel Macron, ya tofa albarkacin bakinsa a yayin rattaba hannu kan yarjejeniyar da Kasar Kenya a fadar gwamnati, gabanin taron ci gaban Afirka da Faransa, domin inganta tare da bunkasar Afirka a Nairobi, ranar 10 ga Mayun 2026.

Macron ya ayyana dala biliyan 27 na zuba jari ga Afirka, yayin da Faransa ke kokarin dakile tasirin China.

Babban jami’in zartarwa na rukunin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya nuna karamci bayan sanya hannu kan kwangilar da kamfanin ‘Sinoma International Engineering’.

Hamshakin attajirin na Nijeriyar, na nazarin yiwuwar zuba hannun jari a bangaren matatun mai a Kasar Kenya, wanda a halin yanzu yake samar da kimanin ganga 650,000 a kowace rana a Nijeriya, matatar mafi girma a duniya.

Dangote ya sha yin gargadin cewa, Afirka na iya fuskantar kasadar zama yankin da ba za su iya amfana da man fetur dinsu ba, idan gwamnatoci suka kasa kare karfin masana’antunsu na cikin gida.

Ya kuma dauki darasi daga Nijeriya, inda matatarsa ta fuskanci kalubale masu nasaba da hanyoyin shigo da mai da hada-hadar ayyukan da a cewar kamfaninsa, na gurgunta tare da raunana karfin jari na dogon lokaci a harkar tace man a cikin gida.

Aikin matatar mai na Gabashin Afirka da aka kiyasta, zai lashe tsakanin dala biliyan 15 zuwa dala biliyan 17, wanda a halin yanzu ake shirin aiwatar da shi a birnin Mombasa na Kasar Kenya.

Dangote
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

MASU ALAKA

Dangote
Labarai

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Dangote
Labarai

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi
Ra'ayi Riga

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Next Post
Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga  Faruku Yabo

Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Dangote

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Dangote

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Dangote

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.