Aliko Dangote na nuni da cewa, zai ci gaba da shirye-shiryen kafa babbar matatar man fetur a gabashin Afirka ne, kadai idan gwamnatocin yankin suka bullo da tsauraran matakan kare matatun mansu, maimakon tataccen man da ake shigowa da shi mai arha daga ketare.
Dangoten, zai ci gaba da tsare-tsaren kafa babbar matatar man ta Gabashin Afirka ne, idan gwamnatocinsu suka bullo da tsauraran matakan kariya a kan man nasu.
Har ila yau, yana da niyyar kafa sabuwar matatar ne, bayan katafariyar cibiyarsa ta Nijeriya, wadda a halin yanzu ita ce matatar man fetur mafi girma a duniya.
Dangote ya yi gargadin cewa, idan ba a yi da gaske ba, Afirka za ta iya zama yankin da ya fi ko’ina tarin mai tare da sayar da shi da arha, tana kuma shigo da tataccen man daga ketare, masana’antunta na cikin gida kuma a lalace.
Ya ba da misali da kalubalen da matatar mai ta Nijeriya ke fuskanta, saboda rashin adalcin tsarin gyaran matatun cikin gida, wanda hakan ke barazana ga zuba jari.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron, ya tofa albarkacin bakinsa a yayin rattaba hannu kan yarjejeniyar da Kasar Kenya a fadar gwamnati, gabanin taron ci gaban Afirka da Faransa, domin inganta tare da bunkasar Afirka a Nairobi, ranar 10 ga Mayun 2026.
Macron ya ayyana dala biliyan 27 na zuba jari ga Afirka, yayin da Faransa ke kokarin dakile tasirin China.
Babban jami’in zartarwa na rukunin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya nuna karamci bayan sanya hannu kan kwangilar da kamfanin ‘Sinoma International Engineering’.
Hamshakin attajirin na Nijeriyar, na nazarin yiwuwar zuba hannun jari a bangaren matatun mai a Kasar Kenya, wanda a halin yanzu yake samar da kimanin ganga 650,000 a kowace rana a Nijeriya, matatar mafi girma a duniya.
Dangote ya sha yin gargadin cewa, Afirka na iya fuskantar kasadar zama yankin da ba za su iya amfana da man fetur dinsu ba, idan gwamnatoci suka kasa kare karfin masana’antunsu na cikin gida.
Ya kuma dauki darasi daga Nijeriya, inda matatarsa ta fuskanci kalubale masu nasaba da hanyoyin shigo da mai da hada-hadar ayyukan da a cewar kamfaninsa, na gurgunta tare da raunana karfin jari na dogon lokaci a harkar tace man a cikin gida.
Aikin matatar mai na Gabashin Afirka da aka kiyasta, zai lashe tsakanin dala biliyan 15 zuwa dala biliyan 17, wanda a halin yanzu ake shirin aiwatar da shi a birnin Mombasa na Kasar Kenya.















Discussion about this post