Tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya jaye daga sake tsayawa takarar komawa majalisar dattawa a karo na biyu domin wakiltar Sakkwato ta Kudu.
Tambuwal wanda ya shugabanci majalisar wakilai ta bakwai ya sadaukar da takararsa ne a jam’iyyar ADC a 2027 ga fitaccen ɗan siyasa Ambasada Faruku Malami Yabo. Yabo, tsohon Kwamishinan kuɗi na Jihar Sakkwato, kuma tsohon Jakadan Nijeriya a ƙasar Jordan yana daga cikin ‘yan takarar da suka fito takarar gwamna a ADC.
Tambuwal wanda ya wakilci mazabar a wa’adin zango ɗaya, ya sadaukar da takarar ne ga Yabo domin saka masa da halacci, da jajircewa da cikakken goyon bayan da yake baiwa siyasarsa a tsayin shekaru.
Magoya bayan jam’iyyar ADC sun jinjinawa tunani da hangen nesan da Tambuwal ya nuna na sadaukar da takararsa lamarin da ba a saba gani ba a siyasar jihar. A na ganin tsayar da Yabo a matsayin ɗan takara wata babbar dubara ce a siyasance da za ta ƙarfafa matsayin jam’iyyar a yankin Sakkwato ta Kudu tare da zama babban kalubale ga jam’iyyar APC musamman a bisa ga zamansa fitaccen ɗan siyasar da ke da tarin magoya baya a faɗin jihar.















Discussion about this post