ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darasin Da Aka Koya Bayan Kammala Kofin Afirka A Morocco

by Abba Ibrahim Wada
7 months ago
Opening Ceremony during the 2025 Africa Cup of Nations AFCON match between Morocco and Comoros at the Prince Moulay Abdellah Stadium in Rabat, Morocco on 21 December 2025 ©Gavin Barker/BackpagePix

Opening Ceremony during the 2025 Africa Cup of Nations AFCON match between Morocco and Comoros at the Prince Moulay Abdellah Stadium in Rabat, Morocco on 21 December 2025 ©Gavin Barker/BackpagePix

Gasar cin kofin Nahiyar Afirka da aka kamala a wannan watan za ta kasance gasar da za a dade ana tattaunawa a kanta na tsawon lokaci saboda yadda aka kare gasar cikin wani yanayi na rashin jin dadi.

Hargitsin da aka samu a lokacin da aka kusa tashi daga wasan karshe, lokacin da bugun fenaritin da aka bai wa Moroko ya kai ga cewa ‘yan wasan Senegal sun fice daga filin wasa, zai kasance abin da za a jima ana magana a kai Kociyan tawagar Moroko, Walid Regragui ya bayyana lamarin a matsayin “abin kunya”, amma har yanzu hukumar kwallon kafa ta Afirka ba ta sanar da wani hukunci ba kan lamarin.

  • Jakadan Sin: Cudanyar Al’adu Za Ta Taimaki Yunkurin Daidaita Hulda Tsakanin Sin Da Amurka
  • Gwamnan Zamfara Ya Yaba Da Gudumawar Ɗan Majalisa Hon. Mai Palace A Bangaren Kiwon Lafiya

Amma kuma rikicin da aka samu a lokacin wasan na karshe bai kamata ya dauke hankulan al’umma daga abubuwa da dama da suka faru a gasar ba, wadda a lokacinta ne aka ci kwallaye mafi yawa.

ADVERTISEMENT

Babu shakka kasar Moroko ta shirya gasa mai kayatarwa, filayen wasan masu kyau, inda filin wasa na Yarima Moulay Abdellah da ke babban birnin kasar ya zama abin kallo ga bakin da suka je kallon gasar

Karbar bakuncin wannan gasa ta AFCON wani bangare ne na shirye-shiryen kasar na karbar bakuncin gasar kofin duniya ta 2030, inda za ta yi hadin gwiwa da Spain da kuma Portugal. Morocco ta zuba jari sosai a baya-bayan nan tare da goyon bayan Sarki

LABARAI MASU NASABA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Mohammed na BI, wanda ya ce kayan da kasar ta samar ya nuna “juriyarta da kuma kwarewa wajen shiri kamar kowace kasa a duniya.

Ana sa ran Morocco za ta kara inganta kayan da ta samar, inda yanzu haka ake shirin yin gyare-gyare ga filin wasa na Mohammed B da ke birnin Casablanca da wasu a biranen Fes da Marrakesh da Agadir – haka nan kuma ake ci gaba da aikin gina filin wasa na Benslimane mai daukar ‘yan kallo dubu dari da sha biyar (115,000).

Shugaban hukumar kwallon kafa ta Kenya, Hussein Mohammed ya amince cewa Moroko ta “ciri tuta” a batun karbar bakuncin gasar, sannan ya ce Kenya na daukar matakan da suka dace domin samar da kayan aiki masu kyau a gasar 2027. Sai dai har yanzu ba a sanar da takamaiman lokacin da za a buga gasar da Kenya da Tanzaniya da kuma Uganda za su dauki bakunci ba.

Hukumar kwallon kafa ta Afirka ta ce kudin da take samu a lokacin gasar sun karu da kimanin kashi 90%, inda kudin tikitin kallon wasa ya taka muhimmiyar rawa, inda ya karu daga dala miliyan 11 a shekarar 2023 a kasar Ibory Coast zuwa dala miliyan 55 a Moroko. Haka nan an samu karin kamfanoni masu daukar nauyi zuwa 23, sannan kuma darajar gasar ta karu sanadiyyar tallata gasar a shafukan sada zumunta. A shekarar da ta gabata hukumar CAF ta yi hasashen samun karin kudaden shiga sama da dala miliyan 114 a lokacin gasar, daga dala miliyan 75 a shekaru biyu da suka gabata.

Daga abubuwa marasa dadi kuwa, an nuna damuwa lokaci zuwa lokaci kan hukunce-hukuncen da alkalan wasa suka zartar. Saboda kafin wasan kusa da na karshe da Nijeriya, ta kai ga cewa har sai da mai horas da Moroko, Walid Regragui ya yi kokarin yayyafa ruwa kan rade-radin da ke cewa alkalan wasa na taimaka wa Moroko.

Babban lamari game da irin wannan takaddama shi ne abin da ya faru a wasan karshe, inda alkalin wasa Jean-Jackues Ndala ya tafiyar da al’amura a tsanake, har sai a kusa da karshen wasan, inda lamurra suka tabarbare cikin kankanin lokaci.

Matakin da alkalin wasan ya dauka na bai wa Moroko bugun fenariti ya sanya wasu sun yi tunanin akwai rashin adalci, lamarin da ya kai ga cewa ‘yan wasa sun fita daga fili.

Amfani da fasahar BAR wajen taimaka wa alkalin wasa a baya-bayan nan ya zamo abu mai rudani, tun bayan amfani da shi da aka yi a 2023.

Sannan kasar Senegal ta nuna damuwa kan rashin tsaro a lokacin da ta isa birnin Rabat, gabanin wasan karshe, inda mutane suka takura su. Sai kuma hatsaniyar da aka samu a cikin filin wasa, inda magoya baya suka yi artabu da jami’an tsaro a lokacin da Moroko ta samu bugun fenariti.

Haka nan an zura ido a ga matakin da hukumar CAF za ta dauka kan abin da ya faru a lokacin da aka ga yaran da ke dakko kwallo a filin wasa na kokarin dauke kyallen mai tsaron raga na Senegal Edouard Mendy.

Sai dai wasu hotunan bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna yadda magoya bayan Moroko ke murna lokacin da aka sace kyallen mai tsaron raga na Nijeriya har sau biyu a lokacin karawar kusa da karshe.

Har ila yau, akwai yiwuwar hukumar CAF ta duba yiwuwar sauya wasu dokokinta kan bayar da katin gargadi a matakin kifa-daya kwala.

Jimillar ‘yan wasa 20 ne suka rika taka-tsantsan a matakin wasan kusa da karshe saboda suna jin tsoron cewa da zarar suka samu katin gargadi, hakan zai hana su buga wasan karshe.

Misali shi ne, kyaftin din Senegal, Kalidou Koulibaly da dan wasan tsakiya Habib Diarra sun gaza buga wasan karshe, kuma irin wannan abu ya kusa faruwa da mai tsaron baya na Nijeriya Calbin Bassey da na Masar

Hossam Abdelmaguid, in da tawagoginsu sun kai wasan na karshe.

Sai dai duk da cewa akwai bukatar ganin an tabbatar da da’a a lokacin gasar, amma masu horarwa da ‘yan wasa da kuma magoya baya har ma da kafofin yada labarai za su ga cewa kwararrun ‘yan wasa sun taka rawa a manyan wasanni kuma nan gaba abubuwa masu kyau da aka gani a wannan gasar za su karu a gasar da za a buga a nan gaba.

Afirka
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

Yaya Toure Na Dab Da Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Next Post
Me Ya Sa Shugabannin Kasashen Turai Suka Yi Ta Ziyartar Kasar Sin?

Me Ya Sa Shugabannin Kasashen Turai Suka Yi Ta Ziyartar Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.