ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon sallar dare (Ƙiyamul-Laili), domin mu saba da tsayuwa a gaban Allah a cikin nutsuwar dare. Dare lokaci ne na sirri tsakanin bawa da Ubangijinsa; lokaci ne da hayaniyar duniya ta lafa, zukata suka natsu, kuma hawaye suka fi kusa da zubowa saboda tsoron Allah da bege gare Shi.

Tsayuwa a gaban Allah da dare tana da wani daɗi na musamman. Ba wai tsayuwar jiki kaɗai ba ce, tsayuwar zuciya ce cikin tawali’u da kaskantar da kai a wurin Allah Ta’ala. A cikin dare, mumini yana furta addu’a cikin sirri, yana neman gafara, yana roƙon rahama, yana kuma bayyana buƙatunsa ba tare da riya ko nuna wa mutane ba.

  • Darussa Daga Ramadan Na 12: Ƙarfafa Alaƙa Da Alƙur’ani A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 11: Sauƙi Da Sassauci A Shari’a

Manzon Allah (SAW) ya bayyana girman ladan wannan ibada a cikin Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim inda ya ce: “Duk wanda ya tsaya ya yi sallar dare a watan Ramalana yana mai imani da neman lada, to an gafarta masa abin da ya gabata na zunubansa”

ADVERTISEMENT

Mai karatu ka lura da sharaɗai biyu kamar haka:

1. Imani; watau a samu cikakkiyar yarda da cewa wannan ibada umarni ce daga Allah.
2. Neman lada; watau bawa ya yin ta domin Allah kaɗai, ba don yabo ko al’ada ba.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

Idan aka haɗa waɗannan biyun, sakamakon shi ne gafara. Wace ni’ima ta fi wannan girma? Mutum ya tsaya a dare yana karanta ayoyi, yana ruku’i da sujada, sai Allah Ya shafe masa abin da ya gabata na kuskure.

Ramalana wata ne da ake raya dare da sallar Tarawihi da Tahajjud. Wannan tarbiyya ce ta ruhi. Domin duk wanda ya saba da tsayuwar dare, zuciyarsa tana samun haske, imaninsa yana ƙaruwa, kuma dangantakarsa da Allah tana ƙarfafa.

Tsayuwar dare tana koya mana:

1. Natsuwa da kame kai, domin ka bar gadonka mai daɗi ka tashi kana ganawa da Mahaliccinka.
2. Sadaukarwa; ka ba wa Allah wani ɓangare na lokacinka mafi daraja.
Sirri da ikhlasi – domin yawanci ana yin ta ne a ɓoye.
3. A haƙiƙa, tsayuwar dare alama ce ta soyayya ga Allah. Domin masoyi yana son ya kasance tare da wanda yake so, ko da a cikin dare ne.

Idan muka ɗanɗani zaƙin tsayuwar dare a Ramalana, to ya kamata mu yi ƙoƙarin ci gaba da wani kaso daga cikinta bayan Ramalana, ko da raka’a biyu ne kafin barci ko bayan tashi. Domin abin da ya fi muhimmanci shi ne dawwama, ba yawa kaɗai ba. Ramalana yana koya mana cewa gafara tana kusa da bayi, rahama tana kusa da su, yardar Allah tana kusa da su, abin da ake so shi ne; a miƙa zuciya gare Shi cikin dare.

Allah Ya sa mu kasance cikin masu tsayuwar dare da imani da neman lada, Ya gafarta mana zunubanmu, Ya haskaka zukatanmu da hasken Alƙur’ani, Ya kuma sa mu zama masu kusanci da Shi a duniya da Lahira. Amin.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Yadda Manyan Taruka Biyu Na Sin Ke Zamowa Madubin Turbar Ci Gaban Kasar

Yadda Manyan Taruka Biyu Na Sin Ke Zamowa Madubin Turbar Ci Gaban Kasar

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.