ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon sallar dare (Ƙiyamul-Laili), domin mu saba da tsayuwa a gaban Allah a cikin nutsuwar dare. Dare lokaci ne na sirri tsakanin bawa da Ubangijinsa; lokaci ne da hayaniyar duniya ta lafa, zukata suka natsu, kuma hawaye suka fi kusa da zubowa saboda tsoron Allah da bege gare Shi.

Tsayuwa a gaban Allah da dare tana da wani daɗi na musamman. Ba wai tsayuwar jiki kaɗai ba ce, tsayuwar zuciya ce cikin tawali’u da kaskantar da kai a wurin Allah Ta’ala. A cikin dare, mumini yana furta addu’a cikin sirri, yana neman gafara, yana roƙon rahama, yana kuma bayyana buƙatunsa ba tare da riya ko nuna wa mutane ba.

  • Darussa Daga Ramadan Na 12: Ƙarfafa Alaƙa Da Alƙur’ani A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 11: Sauƙi Da Sassauci A Shari’a

Manzon Allah (SAW) ya bayyana girman ladan wannan ibada a cikin Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim inda ya ce: “Duk wanda ya tsaya ya yi sallar dare a watan Ramalana yana mai imani da neman lada, to an gafarta masa abin da ya gabata na zunubansa”

ADVERTISEMENT

Mai karatu ka lura da sharaɗai biyu kamar haka:

1. Imani; watau a samu cikakkiyar yarda da cewa wannan ibada umarni ce daga Allah.
2. Neman lada; watau bawa ya yin ta domin Allah kaɗai, ba don yabo ko al’ada ba.

LABARAI MASU NASABA

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Idan aka haɗa waɗannan biyun, sakamakon shi ne gafara. Wace ni’ima ta fi wannan girma? Mutum ya tsaya a dare yana karanta ayoyi, yana ruku’i da sujada, sai Allah Ya shafe masa abin da ya gabata na kuskure.

Ramalana wata ne da ake raya dare da sallar Tarawihi da Tahajjud. Wannan tarbiyya ce ta ruhi. Domin duk wanda ya saba da tsayuwar dare, zuciyarsa tana samun haske, imaninsa yana ƙaruwa, kuma dangantakarsa da Allah tana ƙarfafa.

Tsayuwar dare tana koya mana:

1. Natsuwa da kame kai, domin ka bar gadonka mai daɗi ka tashi kana ganawa da Mahaliccinka.
2. Sadaukarwa; ka ba wa Allah wani ɓangare na lokacinka mafi daraja.
Sirri da ikhlasi – domin yawanci ana yin ta ne a ɓoye.
3. A haƙiƙa, tsayuwar dare alama ce ta soyayya ga Allah. Domin masoyi yana son ya kasance tare da wanda yake so, ko da a cikin dare ne.

Idan muka ɗanɗani zaƙin tsayuwar dare a Ramalana, to ya kamata mu yi ƙoƙarin ci gaba da wani kaso daga cikinta bayan Ramalana, ko da raka’a biyu ne kafin barci ko bayan tashi. Domin abin da ya fi muhimmanci shi ne dawwama, ba yawa kaɗai ba. Ramalana yana koya mana cewa gafara tana kusa da bayi, rahama tana kusa da su, yardar Allah tana kusa da su, abin da ake so shi ne; a miƙa zuciya gare Shi cikin dare.

Allah Ya sa mu kasance cikin masu tsayuwar dare da imani da neman lada, Ya gafarta mana zunubanmu, Ya haskaka zukatanmu da hasken Alƙur’ani, Ya kuma sa mu zama masu kusanci da Shi a duniya da Lahira. Amin.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
Yadda Manyan Taruka Biyu Na Sin Ke Zamowa Madubin Turbar Ci Gaban Kasar

Yadda Manyan Taruka Biyu Na Sin Ke Zamowa Madubin Turbar Ci Gaban Kasar

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.