ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A cikin watan Ramalana muna koyon sallar dare (Ƙiyamul-Laili), domin mu saba da tsayuwa a gaban Allah a cikin nutsuwar dare. Dare lokaci ne na sirri tsakanin bawa da Ubangijinsa; lokaci ne da hayaniyar duniya ta lafa, zukata suka natsu, kuma hawaye suka fi kusa da zubowa saboda tsoron Allah da bege gare Shi.

Tsayuwa a gaban Allah da dare tana da wani daɗi na musamman. Ba wai tsayuwar jiki kaɗai ba ce, tsayuwar zuciya ce cikin tawali’u da kaskantar da kai a wurin Allah Ta’ala. A cikin dare, mumini yana furta addu’a cikin sirri, yana neman gafara, yana roƙon rahama, yana kuma bayyana buƙatunsa ba tare da riya ko nuna wa mutane ba.

  • Darussa Daga Ramadan Na 12: Ƙarfafa Alaƙa Da Alƙur’ani A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 11: Sauƙi Da Sassauci A Shari’a

Manzon Allah (SAW) ya bayyana girman ladan wannan ibada a cikin Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim inda ya ce: “Duk wanda ya tsaya ya yi sallar dare a watan Ramalana yana mai imani da neman lada, to an gafarta masa abin da ya gabata na zunubansa”

ADVERTISEMENT

Mai karatu ka lura da sharaɗai biyu kamar haka:

1. Imani; watau a samu cikakkiyar yarda da cewa wannan ibada umarni ce daga Allah.
2. Neman lada; watau bawa ya yin ta domin Allah kaɗai, ba don yabo ko al’ada ba.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Idan aka haɗa waɗannan biyun, sakamakon shi ne gafara. Wace ni’ima ta fi wannan girma? Mutum ya tsaya a dare yana karanta ayoyi, yana ruku’i da sujada, sai Allah Ya shafe masa abin da ya gabata na kuskure.

Ramalana wata ne da ake raya dare da sallar Tarawihi da Tahajjud. Wannan tarbiyya ce ta ruhi. Domin duk wanda ya saba da tsayuwar dare, zuciyarsa tana samun haske, imaninsa yana ƙaruwa, kuma dangantakarsa da Allah tana ƙarfafa.

Tsayuwar dare tana koya mana:

1. Natsuwa da kame kai, domin ka bar gadonka mai daɗi ka tashi kana ganawa da Mahaliccinka.
2. Sadaukarwa; ka ba wa Allah wani ɓangare na lokacinka mafi daraja.
Sirri da ikhlasi – domin yawanci ana yin ta ne a ɓoye.
3. A haƙiƙa, tsayuwar dare alama ce ta soyayya ga Allah. Domin masoyi yana son ya kasance tare da wanda yake so, ko da a cikin dare ne.

Idan muka ɗanɗani zaƙin tsayuwar dare a Ramalana, to ya kamata mu yi ƙoƙarin ci gaba da wani kaso daga cikinta bayan Ramalana, ko da raka’a biyu ne kafin barci ko bayan tashi. Domin abin da ya fi muhimmanci shi ne dawwama, ba yawa kaɗai ba. Ramalana yana koya mana cewa gafara tana kusa da bayi, rahama tana kusa da su, yardar Allah tana kusa da su, abin da ake so shi ne; a miƙa zuciya gare Shi cikin dare.

Allah Ya sa mu kasance cikin masu tsayuwar dare da imani da neman lada, Ya gafarta mana zunubanmu, Ya haskaka zukatanmu da hasken Alƙur’ani, Ya kuma sa mu zama masu kusanci da Shi a duniya da Lahira. Amin.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Next Post
Yadda Manyan Taruka Biyu Na Sin Ke Zamowa Madubin Turbar Ci Gaban Kasar

Yadda Manyan Taruka Biyu Na Sin Ke Zamowa Madubin Turbar Ci Gaban Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.