ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na (4)

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Darussa

A cikin watan Ramalana muna koyon nisantar algus da yaudara, domin muna tuna cewa Allah Maɗaukaki Yana kallon mu a kowane lokaci. Ba don tsoron mutane muke barin ci da sha da rana ba, domin da ba don girman Allah da lura da kallonsa ba, da mutum zai iya ci ko ya sha a ɓoye ba tare da wani ya sani ba. Amma muminin gaske yana barin hakan ne saboda ya san Allah na ganin sa.

Wannan matsayi shi ake kira Ihsani, watau kai ibada da cikakken sanin cewa kana ƙarƙashin kulawar Allah Yana ganinka. Manzon Allah (S.A.W) ya bayyana ma’anar Ihsani a cikin hadisin da ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Muslim, inda ya ce:
“Ihsani shi ne: ka bauta wa Allah kamar kana ganin Sa; idan kai ba ka ganin Sa, to, Shi Yana ganin ka” Wannan kalma ta ƙunshi asalin gyaran zuciya da tsarkake niyya. Ihsani ba wai kawai yawan ibada ba ne, sai dai ingancinta da tsarkinta ya tattare da ita. Yana nufin ka yi salla da natsuwa, ka yi azumi da gaskiya, ka yi addu’a da tawali’u, ka kuma nisanci saɓo ko da babu mai ganin ka.

  • Darussa Daga Ramadan Na (1)
  • Darussa Daga Ramadan Na (2)

Ramalana wata ne da ke horar da zuciya a kan wannan matsayi. Domin azumi ibada ce ta sirri; babu wanda ya san ko mutum ya karya azuminsa, sanin haka sai shi da Ubangijinsa. Wannan sirrin yana gina wa mumini jin tsoron Allah da kiyaye dokokinsa a fai da ɓoye, da ganin girmansa a zuciya.

ADVERTISEMENT

Idan wannan darasi ya zauna a zuciya, to ba a cikin Ramalana kaɗai zai canza bawa ba, har rayuwar mutum baki ɗaya za ta canza. Zai nisanci algus a kasuwanci, zai guji ha’inci a amanar da aka ɗora masa, zai bar kallon haram da sauraron abin da bai halatta ba, domin ya san cewa Allah na ganin sa.

Ihsani shi ne ginshiƙin kamala a addini. Shi ne mataki mafi girma bayan Musulunci da Imani. Duk wanda ya kai wannan matsayi, zuciyarsa tana rayuwa cikin kulawar Allah, ayyukansa suna cike da tsari da ladabi, rayuwarsa kuma tana cike da haske.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

Saboda haka, Ramalana makaranta ce ta Ihsani. Duk wanda ya koyi darasin nan da gaske, zai fita daga watan nan yana da sabuwar zuciya mai cike tsoron Allah, mai ƙaunar Sa, mai jin daɗin ibada, mai nisantar algus a fili da a ɓoye.

Allah Ya sanya mu cikin bayinsa masu Ihsani, Ya tsarkake zukatanmu, Ya karɓi ibadunmu. Amin.

Darussa
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
An Nuna Shagalin CMG Na Murnar Bikin Bazara A Jiragen Kasa Na Nijeriya

An Nuna Shagalin CMG Na Murnar Bikin Bazara A Jiragen Kasa Na Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.