A cikin watan Ramalana muna koyon nisantar algus da yaudara, domin muna tuna cewa Allah Maɗaukaki Yana kallon mu a kowane lokaci. Ba don tsoron mutane muke barin ci da sha da rana ba, domin da ba don girman Allah da lura da kallonsa ba, da mutum zai iya ci ko ya sha a ɓoye ba tare da wani ya sani ba. Amma muminin gaske yana barin hakan ne saboda ya san Allah na ganin sa.
Wannan matsayi shi ake kira Ihsani, watau kai ibada da cikakken sanin cewa kana ƙarƙashin kulawar Allah Yana ganinka. Manzon Allah (S.A.W) ya bayyana ma’anar Ihsani a cikin hadisin da ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Muslim, inda ya ce:
“Ihsani shi ne: ka bauta wa Allah kamar kana ganin Sa; idan kai ba ka ganin Sa, to, Shi Yana ganin ka” Wannan kalma ta ƙunshi asalin gyaran zuciya da tsarkake niyya. Ihsani ba wai kawai yawan ibada ba ne, sai dai ingancinta da tsarkinta ya tattare da ita. Yana nufin ka yi salla da natsuwa, ka yi azumi da gaskiya, ka yi addu’a da tawali’u, ka kuma nisanci saɓo ko da babu mai ganin ka.
Ramalana wata ne da ke horar da zuciya a kan wannan matsayi. Domin azumi ibada ce ta sirri; babu wanda ya san ko mutum ya karya azuminsa, sanin haka sai shi da Ubangijinsa. Wannan sirrin yana gina wa mumini jin tsoron Allah da kiyaye dokokinsa a fai da ɓoye, da ganin girmansa a zuciya.
Idan wannan darasi ya zauna a zuciya, to ba a cikin Ramalana kaɗai zai canza bawa ba, har rayuwar mutum baki ɗaya za ta canza. Zai nisanci algus a kasuwanci, zai guji ha’inci a amanar da aka ɗora masa, zai bar kallon haram da sauraron abin da bai halatta ba, domin ya san cewa Allah na ganin sa.
Ihsani shi ne ginshiƙin kamala a addini. Shi ne mataki mafi girma bayan Musulunci da Imani. Duk wanda ya kai wannan matsayi, zuciyarsa tana rayuwa cikin kulawar Allah, ayyukansa suna cike da tsari da ladabi, rayuwarsa kuma tana cike da haske.
Saboda haka, Ramalana makaranta ce ta Ihsani. Duk wanda ya koyi darasin nan da gaske, zai fita daga watan nan yana da sabuwar zuciya mai cike tsoron Allah, mai ƙaunar Sa, mai jin daɗin ibada, mai nisantar algus a fili da a ɓoye.
Allah Ya sanya mu cikin bayinsa masu Ihsani, Ya tsarkake zukatanmu, Ya karɓi ibadunmu. Amin.















Discussion about this post