A cikin watan Ramalana, mumini yana koyon miƙa dukkan buƙatunsa da burace-buracensa zuwa ga Allah Maɗaukakin Sarki, saboda girmansa, karamcinsa da yalwar rahamarsa.
Ramalana wata ne na kusanci da Ubangiji, wata ne da ƙofofin alheri suke a buɗe, kuma zuciya take samun tsarkaka, ruhi kuma ya sami wata irin nutsuwa, kuma addu’a ta fi kusa da karɓuwa. Allah Maɗaukaki Yana saka wa bayinsa da suka yi aikin alheri da sakamako mai,. matuƙar an yi aikin da ikhlasi yadda Manzon rahama (S.A.W) ya koyara. Manzon Allah (S.A.W) ya ce: ” Allah Ya ce: Dukkan aikin ɗan’adam nasa ne, sai dai azumi; domin azumi Nawa ne, kuma Ni ne Zan saka masa” Bukhari ne ya ruwaito.
Wannan hadisi mai girma yana nuna mana matsayin azumi a wurin Allah. Azumi ibada ce ta sirri, babu mai sanin haƙiƙanin gaskiyarta sai Allah. Saboda haka Allah Ya keɓe lada da sakamakonta gare Shi kaɗai, alamar girman darajarta da yalwar sakamakonta.
Ramalana wata ne da ya kamata mu haɗa abubuwa uku:
1. Ikhlasi a aiki: watau yin ibada don neman yardar Allah kaɗai, ba don yabo ko gani na mutane ba.
2. Bin dokokin Allah: kiyaye umurninsa da nisantar hane-hanensa, domin ibada ba ta kammala sai da taƙawa.
3. Yawaita addu’a: domin Allah Ya fi kusa da bawansa a wannan wata mai albarka.
Addu’a ita ce makamin mumini. A Ramalana, musamman a lokutan da ake azumi, lokacin buɗa baki, da lokacin yin sahur da cikin Laylatul-Ƙadri, ya dace mumini ya miƙa zuciyarsa gaba ɗaya ga Allah. Ya roƙi gafara, ya roƙi gyaran rayuwarsa, ya roƙi albarka a cikin iyalinsa, ya roƙi shiriya da tsayuwar daka kan addinin Allah Ta’ala.
Abu ne mai matuƙar muhimmanci mu fahimci cewa karɓuwar addu’a tana buƙatar tsarkin zuciya da ci da sha da tufafi na halal. Wanda ya tsarkake zuciyarsa daga hassada, riya da zalunci, ya nisanci haram, ya kuma dage da neman halal, to ya fi kusa da samun amsa addu’a.
Saboda haka, a yi aiki da ikhlasi. A gyara niyya. A riƙe azumi ba kawai da yunwa da ƙishirwa ba, har da azumin idanu, da kunne da harshe. A nisanci gulma da saɓo. A kuma miƙa buƙatu da cikakken yaƙini cewa Allah Mai jin ƙorafi ne, Mai amsa addu’a ne.
Kada mumini ya yanke ƙauna idan bai ga sakamakon addu’arsa nan take ba. Wani lokaci Allah Yana amsa addu’a ta hanyoyi uku: ko Ya ba ka abin da ka roƙa, ko Ya kawar maka da wata masifa makamanciyarta, ko Ya adana maka lada a Lahira. Duk waɗannan alheri ne.
Ramalana wata ne na fata da bushara. Wata ne da Allah Yake karɓar tuba, Yake gafarta zunubai, Ya kuma ɗaukaka darajoji. Don haka ka shiga Ramalana da zuciya mai tawakkali, da harshe mai ambaton Allah, da zuciya mai fatan rahama.
Allah Ya sa mu dace da yin azumi da ikhlasi, Ya karɓi addu’o’inmu, Ya kuma sanya mu cikin bayinsa waɗanda Yake alfahari da su a gaban mala’iku. Amin.















Discussion about this post