Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya yi gargaɗin cewa dawo da tallafin man fetur da Atiku Abubakar ya yi alƙawari zai iya jefa tattalin arziƙin Nijeriya cikin ƙarin matsala.
Sani ya bayyana alƙawarin Atiku na dawo da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027 a matsayin “yaudara”, yana mai cewa Nijeriya ba za ta iya komawa tsohon tsarin biyan tallafin ba.
Ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja, inda ya ce tsohon tsarin tallafin ya janyo asarar maƙudan kuɗaɗen gwamnati tare da ƙara matsalolin cin hanci da fasa-ƙwaurin man fetur.
A cewarsa, komawa tsarin zai ƙara wa gwamnati nauyin kashe kuɗi tare da rage kuɗaɗen da za a iya amfani da su wajen ayyukan raya ƙasa, kiwon lafiya, ilimi da sauran muhimman buƙatun jama’a.
Kalaman Sani na zuwa ne bayan Atiku ya ce ba zai janye shirinsa na dawo da tallafin man fetur ba domin sauƙaƙa wa ‘yan Nijeriya wahalar tsadar rayuwa ba.
Atiku ya bayyana cewa shirinsa zai mayar da hankali kan tallafa wa matatun mai na cikin gida da rage kuɗin samar da man fetur.
Sai dai Sani ya ce ya kamata a nemi wasu hanyoyin rage tsadar rayuwa ba tare da komawa tsohon tsarin biyan tallafin man fetur ba.
Muhawarar kan tallafin man fetur na daga cikin manyan batutuwan da ake sa ran za su mamaye yaƙin neman zaɓen 2027, musamman ganin yadda cire tallafin ya shafi farashin sufuri da kayayyaki a ƙasar.














