Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta hana ‘yan jarida zaman sauraron neman beli na wasu mutum shida da ake zargi da yunƙurin juyin mulki a ga gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu.
Jami’an kotu, tare da goyon bayan jami’an DSS, sun umarci ‘yan jarida da su fice daga cikin ɗakin shari’ar jim kaɗan kafin alƙali mai shari’ar, Joyce Abdulmalik, ta shiga zaman.
Wani jami’in kotu da ya buƙaci a sakaye sunansa ya shaida wa ‘yan jarida cewa umarnin ya zo ne daga alƙaliyar, yayin da wani jami’in DSS ya ce za a bayar da bayani daga baya, saboda haka, ‘yan jaridar suka bi umarnin suka fice nan take.
Ƴan jarida daga kafafen yaɗa labarai daban-daban sun isa kotun tun da misalin ƙarfe 8:00 na safe, amma aka tilasta musu fita da misalin 9:07 na safe bayan wannan umarni.
Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da jama’a ke mayar da hankali kan shari’ar ta mutum shida da Gwamnatin Tarayya ta gurfanar a gaban kotu a makon da ya gabata, bisa zargin yunƙurin juyin mulki ko bayar da gudummawar nasararsa.















Discussion about this post