Rundunar Ƴansandan ta ƙasa a jihar Kogi ta tabbatar da ceto ɗalibai 17 bayan harin satar mutane da aka kai makarantar Daarul Kitab da ke Lokoja.
Lamarin ya faru ne da daren Lahadi, 26 ga Afrilu, 2026, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai farmaki makarantar da ke Zariagi, tare da sace mutane 26, ciki har da ɗalibai 24 da mata biyu na mai makarantar.
Jami’in ‘yansanda ya bayyana cewa an tura haɗaɗɗiyar rundunar jami’an tsaro nan take bayan samun rahoto, inda suka fara aikin ceto wanda ya kai ga kubutar da ɗalibai 17 daga cikin waɗanda aka sace.
A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da ƙoƙarin ceto sauran mutum 9, ɗalibai 7 da mata biyu ta hanyar sintiri, da binciken dazuzzuka, da tattara bayanan sirri domin cafke masu laifi.
Kwamishinan ‘yansanda na jihar, CP Naziru Bello Kankarofi, ya ziyarci wurin da abin ya faru tare da umartar ƙarin tura jami’an musamman domin ƙarfafa aikin ceto.
Rundunar ta buƙaci al’umma su kasance masu natsuwa tare da taimakawa jami’an tsaro da sahihan bayanai, tana mai jaddada aniyarta ta kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.















Discussion about this post