Hukumar ilimin bai ɗaya ta Jihar Yobe tare da haɗin gwiwar Hukumar ilimin bai ɗaya (UBEC), ta ƙaddamar da raba kayan koyarwa da Malaman makaranta suke amfani da su, da kuma waɗanda aka ba masu koyo a ƙarƙashi tsarin taimako na shekarar karatu ta 2024/2025 a duk makarantun da suke a faɗin Jihar.
Raba kayan an yi shi ne a wurin da Hukumar SUBEB ta Yobe ta ke ajiye kayan ta a Damaturu, an yi hakan ne domin a samu damar ingantawa da bunƙasa kayan koyarwa da na Malamai masu inganci a makarantun da suke tsarin makarantu du faɗin Jihar .
Da yake nashi jawabin wajen buɗe taron ƙaddamar da raba kayan aiki kwamishinan, ilimi da ilimin bai ɗaya da Sakandare, Farfesa Abba Adam Idris, ya ce samar da kayan aiki ya nuna irin damuwar da Gwamnatin Jihar Yobe ta yi da kuma Hukumar ilimin bai ɗaya, domin su bunƙasa bangaren ilimi da yadda za a riƙa samun sakamako mai inganci a duk faɗin makarantun Jihar
Farfesa Idris ya yi kira da Hedimastoci, da masu tafiyar da mulkin makarantu, har ma da masu ruwa da tsaki da su tabbatar da ana adalci, gaskiya,a lokacin da ake raba su kayan ga makarantun da za a kai ma su.
Shugaban hukumar ilimiin bai ɗaya ta Jihar Yobe SUBEB, Umaru Hassan Babayo lokacin da yake na shi jawabin ya miƙa godiyar sa zuwa ga Gwamna Mai Mala Buni saboda yadda yake ci gaba da ba bangaren ilimi taimako, musamman ma maganar ɗaukar sabbin Malaman makarantar da ya yi, domin ya bunƙasa ilimi ya kasance mai nagarta ta hanyar koyarwa, da kuma koyo a makarantu.
Babayo ya yi kira da Malaman makaranta su ƙara ƙaimi wajen taimakawa gwamnati domin ta samu cimma burin ta na bunƙasar ilimi musamman ma su ƴan makaranta waɗanda ake koya mawa.
Shi ma da yake na shi jawabin Shugaban kwamitin ilimi, Digma Maina Gana, ya yi kira da Hedimastoci su tabbatar da kowane Malami ya na zuwa makaranta .
Ya yi kira da Sakatarorin ilimi su maida hankalin su ga sa ido akan yadda aka tafiyar da ayyukan koyarwa a makarantun su.
A na shi jawabin,darektan shiyya, na UBEC Abdullahi Mohammed Jarma, cwa ya yi ilimi ya dogara ne ga samuwar kayan aikin da suka dace, ƙwararrun Malaman da suka san kan su, su ma masu koyon za a san yadda za a ja ra’ayin su domin su koya.















Discussion about this post