ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farfesa Gwarzo Ya Gwangwaje Cibiyar Ilimi ‘Alliance Française Kano’ Da Gini Mai Hawa Biyu Na Zamani

...ya kuma bayar da tallafin Naira Miliyan 10 na gudanarwa

by Bello Hamza and Sulaiman
6 months ago
Gwarzo

Wanda ya kafa gamayyar jami’o’in MAAUN, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, ya bai wa cibiyar ilimin koyon harshen faransanci ta ‘Alliance Française Kano’ ginin bene mai hawa biyu ɗauke da dukkan kayan aiki na zamani—ciki har da ajujuwan karatu na zamani, dakunan koyon harshe na zamani, dakunan sauraro da nune-nune harshe, da kujeru da tebura na musamman da aka tsara don inganta koyarwa.

Fitaccen mai bunkasa harkokin ilimin ya ƙara tabbatar da irin jajircewarsa wajen bunƙasa ilimi da kuma musayar al’adu, ta hanyar ƙara bayar da tallafin Naira miliyan 10 domin gudanar da ayyukan yau da kullum da kuma tabbatar da dorewar cibiyar.

  • Sin Ta Ce Ikirarin Japan Cewa Matsayarta Kan Batun Taiwan Ba Ta Sauya Ba, Bai Wadatar Ba
  • Martabar Kasar Sin Na Karuwa A Idanun Duniya

Ginin da jakadan Faransa a Nijeriya, Marc Fonbaustier, tare da Farfesa Gwarzo suka kaddamar da shi ga al’umma, ya ƙunshi allunan koyarwa na zamani, na’urar intanet mai ƙarfi, ɗakunan taro, kayan koyar wa da ke amfani da sauti da hoto, da kuma dakunan karatu na dijital.

ADVERTISEMENT

 

Ginin da ke Ahmadiyya Junction a kan titin filin jirgin sama na Kano, yanzu ana ɗaukarsa a matsayin ɗaya daga cikin cibiyoyin koyar da harshen Faransanci da al’adu a zamance a Arewacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

 

A cewar Farfesa Gwarzo, kafa irin wannan cibiya ta zamani zai taka rawar gani wajen farfaɗo da ilimin harsuna biyu a Kano, tare da bai wa ɗalibai damar samun ingantaccen horo na harshen Faransanci a matakin duniya.

 

A jawabinsa, Jakadan Faransa a Nijeriya, Marc Fonbaustier, ya yaba wa Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo bisa kyautar ginin da kuma samar da gagarumin kayayyakin da aka tanada a ciki.

 

Jakadan ya yi addu’ar Allah Ya kara wa Farfesa Gwarzo tsawon rai da lafiya, domin ya cigaba da bayar da irin wannan gudummawa ta jinƙai da kuma bunkasa ilimi wanda ya shahara da su.

 

Daraktan Alliance Française Kano, Ali Dabo, ya bayyana matukar godiyarsa ga Farfesa Gwarzo bisa ginin da kuma kayayyakin zamani da ya samar.

 

Ya ce a tsawon shekarun da cibiyar ta fara aiki a Kano, babu wani mutum da ya taɓa gyara wa ko sauya tsarin cibiyar, balle ɗaukaka ta zuwa wannan mataki na musamman kamar yadda Farfesa Gwarzo ya yi.

 

Ya ƙara da cewa, Farfesa Gwarzo ya kawo ƙarshen dogon lokacin da cibiyar ta shafe tana zaman haya fiye da shekara goma, ta hanyar samar mata da ofishi na dindindin kuma mai daraja.

Gwarzo
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja
Gwarzo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Mbappe

Mbappe Ya Kafa Wani Sabon Tarihi A Gasar Zakarun Turai

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.