ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Farfesa Gwarzo Ya Gwangwaje Cibiyar Ilimi ‘Alliance Française Kano’ Da Gini Mai Hawa Biyu Na Zamani

...ya kuma bayar da tallafin Naira Miliyan 10 na gudanarwa

by Bello Hamza and Sulaiman
7 months ago
Gwarzo

Wanda ya kafa gamayyar jami’o’in MAAUN, Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, ya bai wa cibiyar ilimin koyon harshen faransanci ta ‘Alliance Française Kano’ ginin bene mai hawa biyu ɗauke da dukkan kayan aiki na zamani—ciki har da ajujuwan karatu na zamani, dakunan koyon harshe na zamani, dakunan sauraro da nune-nune harshe, da kujeru da tebura na musamman da aka tsara don inganta koyarwa.

Fitaccen mai bunkasa harkokin ilimin ya ƙara tabbatar da irin jajircewarsa wajen bunƙasa ilimi da kuma musayar al’adu, ta hanyar ƙara bayar da tallafin Naira miliyan 10 domin gudanar da ayyukan yau da kullum da kuma tabbatar da dorewar cibiyar.

  • Sin Ta Ce Ikirarin Japan Cewa Matsayarta Kan Batun Taiwan Ba Ta Sauya Ba, Bai Wadatar Ba
  • Martabar Kasar Sin Na Karuwa A Idanun Duniya

Ginin da jakadan Faransa a Nijeriya, Marc Fonbaustier, tare da Farfesa Gwarzo suka kaddamar da shi ga al’umma, ya ƙunshi allunan koyarwa na zamani, na’urar intanet mai ƙarfi, ɗakunan taro, kayan koyar wa da ke amfani da sauti da hoto, da kuma dakunan karatu na dijital.

ADVERTISEMENT

 

Ginin da ke Ahmadiyya Junction a kan titin filin jirgin sama na Kano, yanzu ana ɗaukarsa a matsayin ɗaya daga cikin cibiyoyin koyar da harshen Faransanci da al’adu a zamance a Arewacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

 

A cewar Farfesa Gwarzo, kafa irin wannan cibiya ta zamani zai taka rawar gani wajen farfaɗo da ilimin harsuna biyu a Kano, tare da bai wa ɗalibai damar samun ingantaccen horo na harshen Faransanci a matakin duniya.

 

A jawabinsa, Jakadan Faransa a Nijeriya, Marc Fonbaustier, ya yaba wa Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo bisa kyautar ginin da kuma samar da gagarumin kayayyakin da aka tanada a ciki.

 

Jakadan ya yi addu’ar Allah Ya kara wa Farfesa Gwarzo tsawon rai da lafiya, domin ya cigaba da bayar da irin wannan gudummawa ta jinƙai da kuma bunkasa ilimi wanda ya shahara da su.

 

Daraktan Alliance Française Kano, Ali Dabo, ya bayyana matukar godiyarsa ga Farfesa Gwarzo bisa ginin da kuma kayayyakin zamani da ya samar.

 

Ya ce a tsawon shekarun da cibiyar ta fara aiki a Kano, babu wani mutum da ya taɓa gyara wa ko sauya tsarin cibiyar, balle ɗaukaka ta zuwa wannan mataki na musamman kamar yadda Farfesa Gwarzo ya yi.

 

Ya ƙara da cewa, Farfesa Gwarzo ya kawo ƙarshen dogon lokacin da cibiyar ta shafe tana zaman haya fiye da shekara goma, ta hanyar samar mata da ofishi na dindindin kuma mai daraja.

Gwarzo
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
Gwarzo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
Mbappe

Mbappe Ya Kafa Wani Sabon Tarihi A Gasar Zakarun Turai

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.