ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasa-kwaurin Abinci: Gwamnati Ta Cafke Motocin Dakon Hatsi 141

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Abinci

A ci gaba da daukar matakan shawo kan hauhawar farashin abinci da tsadar rayuwa, Gwamnatin Tarayyar Nijeriya a ranar Talata ta ce ta cafke wasu manyan motoci 141 da ke yunkurin safarar hatsi da sauran kayayyakin abinci zuwa Kasashen Jamhuriyar Nijar, Chadi, Kamaru, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

Kwanturolan Hukumar Hana Fasa Kwauri na Nijeriya, Bashir Adeniyi, ya ce a cikin makonni biyu hukumar ta kama kimanin tireloli 120 da suka yi safarar kayan abinci daga Nijeriya, yayin da Hukumar EFCC ta hana manyan motocin abinci 21 barin kasar.

  • Kabilanci Da Magudin Zabe Ke Kassara Samun Shugabanci Nagari – Jonathan
  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika

A yayin da Kwanturola Janar Na Hukumar ke bayyana matakan da ake dauka na tabbatar da wadatar abinci a majalisar wakilai da ke Abuja, direbobin manyan motocin da ke fuskantar hare-haren bata gari don kwashe kayan abinci, sun yi barazanar cewa za su shiga yajin aiki idaka ci gaba hana su aikinsu.

ADVERTISEMENT

Motoci da ma’ajiyar kaya da dama mallakin masana’antu da sauran ma’aikatu masu zaman kansu sun fuskanci hare-hare daga wasu bata gari yayin da hauhawar farashin kayan abinci da kuma tsadar rayuwa ke kara kamari a kasar.

Ko a makon da ya gabata ma wasu matasa suka daka wa wasu manyan motocin dakon kayan abinci wawa da suka makale a tsakanin hanyar Kaduna zuwa Suleja ta Jihar Neja.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sannan an kai hari a wani rumbun ajiyar kaya na Sakatariyar Noma da Raya Karkara ta Gwamnatin Tarayya da ke unguwar Dei-Dei a Babban Birnin Tarayya inda suka yi awon gaba da shinkafa da hatsi da sauran kayayyakin agaji.

Kazalika wasu bata-gari sun sake kai farmaki wani rumbum ajiyar kaya da ke unguwar Idu Industrial Estate, Jabi, Abuja, amma sojojin da ke gadin ginin sun dakile shirin nasu.

Bugu da kari, wasu matasa sun kai hari kan motocin da ke jigilar kayayyakin gini da wata mota dauke da taliyar spaghetti a jihohin Ogun da Kaduna.

Cikin nuna damuwa da ci gaban da aikata abubuwan da ba su dace ba, kungiyoyi masu zaman kansu sun yi gargadin cewa hare-haren na iya haifar da rufe masana’antu a duk fadin kasar.

Da yake yi wa ’yan majalisar tarayya bayani kan aiwatar da umarnin da shugaban kasa ya bayar na dakile safarar abinci a lokacin ganawar tasu, Shugaban Hukumar Kwastam, Adeniyi, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin a karkatar da manyan motocin da aka kama zuwa kasuwannin yankin da suke wadanda an kama su ne domin kawo karshen hauhawar farashin hatsi da sauran kayan abinci.

Manyan motocin dakon abinci 120

“A cikin makonni biyu mun cafke kimanin tireloli 120 na kayan abinci da za su fita daga kasar. Wadannan su ne kayan abinci da shugaban kasa ya bukaci mu mayar wa kasuwannin cikin gida. Mun yi imanin hakan zai rage hauhawar farashin kayan abinci a wadannan wuraren,” in ji shi.

Ya ce an yanke shawarar dakatar da safarar kayan abinci ne domin a yaki yunwa da kuma dakatar da masu karfafa wa masu son arzuta kansu da dukiyar al’umma.

Ya kuma yi gargadi kan daukar matakan gaggawa don magance matsalar karancin abinci da ake fama da ita a kasar, inda ya kara da cewa dole ne kasar ta dauki matakai na dogon lokaci domin shawo kan lamarin.

Adeniyi ya bayyana cewa hukumar kwastam na taka rawar gani wajen ganin an shawo kan matsalar samar da abinci, inda ya kara da cewa a halin yanzu galibin abubuwan da ake amfani da su na noma suna jawo rashin biyan haraji da karin haraji.

Kwanturolan ya lura cewa bukatar darasin da aka koya a lokacin da ake gwanjon kayan abinci da aka kama a Legas shi ya sa hukumar ta fara aiwatar da shirin a wajen Jihar Legas.

Kimanin mutum bakwai ne suka mutu sakamakon turmutsitsin da ya barke a shalkwatar hukumar NCS da ke unguwar Yaba a Jihar Legas a lokacin da ake gwanjon buhunan shinkafa da Hukumar NCS ta kwace a hannun masu fasa kwauri a watan jiya.

Lamarin ya tilastawa hukumomi dakatar da gudanar da aikin.

Da yake jawabi ga ’yan majalisar kan yadda za a yi gwanjon kayan ga jama’a, Adeniyi ya ce, Shugaba Tinubu ya umurci hukumar NCS ta yi gwanjon kayan ga marasa galihu a Nijeriya, yana mai cewa an fara aiwatar da shirin ne a Legas, amma daga baya aka hana.

Adeniyi ya ci gaba da cewa, kayayyakin abincin da aka kama za a sayar da su ne a kasuwannin cikin gida a fadin kasar nan bisa umarnin shugaban kasa.

Adeniyi ya ci gaba da cewa, abincin da aka kama za a sayar dasu ne a sauka cikin gida a fadin kasar nan bisa tsarin kasa.

Ya ce, “Shugaban kasa ya ba da umarnin mu sayar wa ‘yan Nijeriya mabukata kayan abinci da aka kama wadanda ake samarwa a cikin gida kai tsaye. Wannan yana daya daga cikin hanyoyin magance yunwa da karancin abinci da muke fuskanta, kuma mun fara wannan aiwatar da wannan aiki a Legas.

Abinci
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Afirka

An Yi Taron Dandalin Tattaunawa Tsakanin Kwararrun Sin Da Afirka A Tanzaniya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.