ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasa-kwaurin Abinci: Gwamnati Ta Cafke Motocin Dakon Hatsi 141

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Abinci

A ci gaba da daukar matakan shawo kan hauhawar farashin abinci da tsadar rayuwa, Gwamnatin Tarayyar Nijeriya a ranar Talata ta ce ta cafke wasu manyan motoci 141 da ke yunkurin safarar hatsi da sauran kayayyakin abinci zuwa Kasashen Jamhuriyar Nijar, Chadi, Kamaru, da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

Kwanturolan Hukumar Hana Fasa Kwauri na Nijeriya, Bashir Adeniyi, ya ce a cikin makonni biyu hukumar ta kama kimanin tireloli 120 da suka yi safarar kayan abinci daga Nijeriya, yayin da Hukumar EFCC ta hana manyan motocin abinci 21 barin kasar.

  • Kabilanci Da Magudin Zabe Ke Kassara Samun Shugabanci Nagari – Jonathan
  • An Rufe Taron Koli Na Kafofin Yada Labarai Dangane Da Kwaikwayon Hazikancin Dan Adam A Afrika

A yayin da Kwanturola Janar Na Hukumar ke bayyana matakan da ake dauka na tabbatar da wadatar abinci a majalisar wakilai da ke Abuja, direbobin manyan motocin da ke fuskantar hare-haren bata gari don kwashe kayan abinci, sun yi barazanar cewa za su shiga yajin aiki idaka ci gaba hana su aikinsu.

ADVERTISEMENT

Motoci da ma’ajiyar kaya da dama mallakin masana’antu da sauran ma’aikatu masu zaman kansu sun fuskanci hare-hare daga wasu bata gari yayin da hauhawar farashin kayan abinci da kuma tsadar rayuwa ke kara kamari a kasar.

Ko a makon da ya gabata ma wasu matasa suka daka wa wasu manyan motocin dakon kayan abinci wawa da suka makale a tsakanin hanyar Kaduna zuwa Suleja ta Jihar Neja.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Sannan an kai hari a wani rumbun ajiyar kaya na Sakatariyar Noma da Raya Karkara ta Gwamnatin Tarayya da ke unguwar Dei-Dei a Babban Birnin Tarayya inda suka yi awon gaba da shinkafa da hatsi da sauran kayayyakin agaji.

Kazalika wasu bata-gari sun sake kai farmaki wani rumbum ajiyar kaya da ke unguwar Idu Industrial Estate, Jabi, Abuja, amma sojojin da ke gadin ginin sun dakile shirin nasu.

Bugu da kari, wasu matasa sun kai hari kan motocin da ke jigilar kayayyakin gini da wata mota dauke da taliyar spaghetti a jihohin Ogun da Kaduna.

Cikin nuna damuwa da ci gaban da aikata abubuwan da ba su dace ba, kungiyoyi masu zaman kansu sun yi gargadin cewa hare-haren na iya haifar da rufe masana’antu a duk fadin kasar.

Da yake yi wa ’yan majalisar tarayya bayani kan aiwatar da umarnin da shugaban kasa ya bayar na dakile safarar abinci a lokacin ganawar tasu, Shugaban Hukumar Kwastam, Adeniyi, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin a karkatar da manyan motocin da aka kama zuwa kasuwannin yankin da suke wadanda an kama su ne domin kawo karshen hauhawar farashin hatsi da sauran kayan abinci.

Manyan motocin dakon abinci 120

“A cikin makonni biyu mun cafke kimanin tireloli 120 na kayan abinci da za su fita daga kasar. Wadannan su ne kayan abinci da shugaban kasa ya bukaci mu mayar wa kasuwannin cikin gida. Mun yi imanin hakan zai rage hauhawar farashin kayan abinci a wadannan wuraren,” in ji shi.

Ya ce an yanke shawarar dakatar da safarar kayan abinci ne domin a yaki yunwa da kuma dakatar da masu karfafa wa masu son arzuta kansu da dukiyar al’umma.

Ya kuma yi gargadi kan daukar matakan gaggawa don magance matsalar karancin abinci da ake fama da ita a kasar, inda ya kara da cewa dole ne kasar ta dauki matakai na dogon lokaci domin shawo kan lamarin.

Adeniyi ya bayyana cewa hukumar kwastam na taka rawar gani wajen ganin an shawo kan matsalar samar da abinci, inda ya kara da cewa a halin yanzu galibin abubuwan da ake amfani da su na noma suna jawo rashin biyan haraji da karin haraji.

Kwanturolan ya lura cewa bukatar darasin da aka koya a lokacin da ake gwanjon kayan abinci da aka kama a Legas shi ya sa hukumar ta fara aiwatar da shirin a wajen Jihar Legas.

Kimanin mutum bakwai ne suka mutu sakamakon turmutsitsin da ya barke a shalkwatar hukumar NCS da ke unguwar Yaba a Jihar Legas a lokacin da ake gwanjon buhunan shinkafa da Hukumar NCS ta kwace a hannun masu fasa kwauri a watan jiya.

Lamarin ya tilastawa hukumomi dakatar da gudanar da aikin.

Da yake jawabi ga ’yan majalisar kan yadda za a yi gwanjon kayan ga jama’a, Adeniyi ya ce, Shugaba Tinubu ya umurci hukumar NCS ta yi gwanjon kayan ga marasa galihu a Nijeriya, yana mai cewa an fara aiwatar da shirin ne a Legas, amma daga baya aka hana.

Adeniyi ya ci gaba da cewa, kayayyakin abincin da aka kama za a sayar da su ne a kasuwannin cikin gida a fadin kasar nan bisa umarnin shugaban kasa.

Adeniyi ya ci gaba da cewa, abincin da aka kama za a sayar dasu ne a sauka cikin gida a fadin kasar nan bisa tsarin kasa.

Ya ce, “Shugaban kasa ya ba da umarnin mu sayar wa ‘yan Nijeriya mabukata kayan abinci da aka kama wadanda ake samarwa a cikin gida kai tsaye. Wannan yana daya daga cikin hanyoyin magance yunwa da karancin abinci da muke fuskanta, kuma mun fara wannan aiwatar da wannan aiki a Legas.

Abinci
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Afirka

An Yi Taron Dandalin Tattaunawa Tsakanin Kwararrun Sin Da Afirka A Tanzaniya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.