A ranar Talata hukumar kwallon kafa ta FIFA ta kara yawan kudin da za ta bai wa kasashen dake buga gasar cin kofin Duniya zuwa kusan Dala miliyan 900 bayan samun karin kudaden shiga da hukumar kwallon ta yi, tun da farko kasashen sun nuna damuwa game da karuwar kudaden da suke kashewa da suka hada da kudin Otal, Zirga-zirga da Alawus-alawus na ‘yan wasa.
Hukumar kwallon kafa ta Duniya ta ce a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa kudaden da aka raba wa kasashe 48 da za su halarci gasar cin kofin Duniya da za a buga a kasashen Medico, Canada da Amurka za su haura Dala miliyan 871, fiye da Dala 724 da aka ware tun bayan sanarwar a watan Disamba.
An sanar da karin kudaden a wani zama da FIFA ta yi kafin taron kwamitin gudanarwa na hukumar da za a yi a Bancouber ranar Alhamis, an samu karuwar kudin ne bayan da aka ruwaito cewa mambobin FIFA da dama sun yi korafi akan cewa tsadar tafiye-tafiye, haraji da sauran ayyuka na iya haifar da asarar kudin shiga ga hukumar da ke shirya gasar, yanzu hukumar ta kara kudaden da Dala miliyan 2.5 ga kowace kasa da ta cancanci shiga gasar.
Ana sa ran FIFA za ta sami kusan Dala biliyan 13 daga wannan kofin Duniya na bana da za a buga wanda shi ne karo na farko da kasashe 48 za su buga gasar, ita ce mafi girma a gasar cin kofin Duniya a tarihi, kudin da FIFA za ta bayar a bana ya karu da kashi 50 cikin 100 fiye da wadanda ta bayar a shekarar 2022, karin kudaden ya zo ne yayin da FIFA ke kara fuskantar suka game da tsadar tikitin shiga gasar, yayin da wasu hukumomi a Amurka suka kara farashin sufuri sosai yayin da gasar ke karatowa.















Discussion about this post