Jam’iyyar ADC ta bayyana cewa za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen duk gari na 2027, tana mai watsi da jita-jitar da ke cewa ba za ta shiga zaɓen ba, inda ta bayyana zantukan a matsayin marasa tushe.
Jam’iyyar ta ce duk da abin da ta kira “sabbin rikice-rikice,” tana nan daram kan burinta na ceto Nijeriya daga abin da ta bayyana a matsayin rashin kyakkyawan shugabanci na jam’iyyar APC, tare da hana ƙasar fadawa tsarin jam’iyya ɗaya.
A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, ADC ta bayyana rahotannin da ke cewa ba za ta gabatar da ‘yan takara ba a 2027 a matsayin “marasa tushe ba tare da hujja ba.”
Jam’iyyar ta jaddada cewa a shirye take tsaf domin shiga zaɓen, tana mai cewa tana aiki tukuru domin gabatar da ‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma waɗanda za su samu karɓuwa a matakin ƙasa baki ɗaya.
Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar ADC na so ta bayyana a sarari cewa muna nan kan ƙudurinmu na ceto Nijeriya daga gazawar gwamnatin APC da kuma hana ƙasar shiga tsarin jam’iyya ɗaya mai haɗari.”
Ta ƙara da cewa: “Mun lura da jita-jitar da ke cewa ADC ba za ta fitar da ‘yan takara a zaɓen 2027 ba. Muna ganin irin waɗannan maganganu a matsayin marasa tushe, na yaudara, kuma an yi su ne domin haddasa ruɗani ba tare da wani dalili ba.”
Jam’iyyar ta sake jaddada cewa babu wani cikas na doka da zai hana ta shiga zaɓen 2027, tana mai cewa tana bin dukkan tanade-tanaden kundin tsarin mulki da dokar zaɓe.
“Mu fayyace: ADC za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen 2027—‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma masu karɓuwa a faɗin ƙasa waɗanda za su iya jagorantar ƙasar nan daga halin da take ciki,” in ji sanarwar.
Jam’iyyar ta kuma bayyana kanta a matsayin babbar jam’iyyar adawa, tana mai mai da hankali kan haɗa kan ‘yan Nijeriya da gina tsari mai ƙarfi domin samun nasara a zaɓe.
“Ba mu damu da surutu ba. Muna mai da hankali kan ainihin aiki—shirya jama’a a faɗin ƙasa, jawo hankalin ‘yan Nijeriya da suka gaji da rashin tsaro, tsadar rayuwa, da ƙarancin damar rayuwa, tare da gina tsarin da ba wai kawai zai ba mu damar tsayawa takara ba, har ma da cin zaɓe,” in ji jam’iyyar.
ADC ta buƙaci mambobinta, magoya bayanta, da sauran jama’a da su yi watsi da abin da ta kira jita-jita marasa tushe, tana mai cewa aikin da ke gaba na buƙatar haɗin kai da jajircewa, ba zato-zato ba.















Discussion about this post