ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Gabatar Da ‘Yan Takara A Kowacce Kujera A Zaɓen 2027 — ADC

by Muhammad
3 months ago

Jam’iyyar ADC ta bayyana cewa za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen duk gari na 2027, tana mai watsi da jita-jitar da ke cewa ba za ta shiga zaɓen ba, inda ta bayyana zantukan a matsayin marasa tushe.

Jam’iyyar ta ce duk da abin da ta kira “sabbin rikice-rikice,” tana nan daram kan burinta na ceto Nijeriya daga abin da ta bayyana a matsayin rashin kyakkyawan shugabanci na jam’iyyar APC, tare da hana ƙasar fadawa tsarin jam’iyya ɗaya.

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, ADC ta bayyana rahotannin da ke cewa ba za ta gabatar da ‘yan takara ba a 2027 a matsayin “marasa tushe ba tare da hujja ba.”

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta jaddada cewa a shirye take tsaf domin shiga zaɓen, tana mai cewa tana aiki tukuru domin gabatar da ‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma waɗanda za su samu karɓuwa a matakin ƙasa baki ɗaya.

Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar ADC na so ta bayyana a sarari cewa muna nan kan ƙudurinmu na ceto Nijeriya daga gazawar gwamnatin APC da kuma hana ƙasar shiga tsarin jam’iyya ɗaya mai haɗari.”

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Ta ƙara da cewa: “Mun lura da jita-jitar da ke cewa ADC ba za ta fitar da ‘yan takara a zaɓen 2027 ba. Muna ganin irin waɗannan maganganu a matsayin marasa tushe, na yaudara, kuma an yi su ne domin haddasa ruɗani ba tare da wani dalili ba.”

Jam’iyyar ta sake jaddada cewa babu wani cikas na doka da zai hana ta shiga zaɓen 2027, tana mai cewa tana bin dukkan tanade-tanaden kundin tsarin mulki da dokar zaɓe.

“Mu fayyace: ADC za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen 2027—‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma masu karɓuwa a faɗin ƙasa waɗanda za su iya jagorantar ƙasar nan daga halin da take ciki,” in ji sanarwar.

Jam’iyyar ta kuma bayyana kanta a matsayin babbar jam’iyyar adawa, tana mai mai da hankali kan haɗa kan ‘yan Nijeriya da gina tsari mai ƙarfi domin samun nasara a zaɓe.

“Ba mu damu da surutu ba. Muna mai da hankali kan ainihin aiki—shirya jama’a a faɗin ƙasa, jawo hankalin ‘yan Nijeriya da suka gaji da rashin tsaro, tsadar rayuwa, da ƙarancin damar rayuwa, tare da gina tsarin da ba wai kawai zai ba mu damar tsayawa takara ba, har ma da cin zaɓe,” in ji jam’iyyar.

ADC ta buƙaci mambobinta, magoya bayanta, da sauran jama’a da su yi watsi da abin da ta kira jita-jita marasa tushe, tana mai cewa aikin da ke gaba na buƙatar haɗin kai da jajircewa, ba zato-zato ba.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.