ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Gabatar Da ‘Yan Takara A Kowacce Kujera A Zaɓen 2027 — ADC

by Muhammad
4 months ago

Jam’iyyar ADC ta bayyana cewa za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen duk gari na 2027, tana mai watsi da jita-jitar da ke cewa ba za ta shiga zaɓen ba, inda ta bayyana zantukan a matsayin marasa tushe.

Jam’iyyar ta ce duk da abin da ta kira “sabbin rikice-rikice,” tana nan daram kan burinta na ceto Nijeriya daga abin da ta bayyana a matsayin rashin kyakkyawan shugabanci na jam’iyyar APC, tare da hana ƙasar fadawa tsarin jam’iyya ɗaya.

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, ADC ta bayyana rahotannin da ke cewa ba za ta gabatar da ‘yan takara ba a 2027 a matsayin “marasa tushe ba tare da hujja ba.”

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta jaddada cewa a shirye take tsaf domin shiga zaɓen, tana mai cewa tana aiki tukuru domin gabatar da ‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma waɗanda za su samu karɓuwa a matakin ƙasa baki ɗaya.

Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar ADC na so ta bayyana a sarari cewa muna nan kan ƙudurinmu na ceto Nijeriya daga gazawar gwamnatin APC da kuma hana ƙasar shiga tsarin jam’iyya ɗaya mai haɗari.”

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ta ƙara da cewa: “Mun lura da jita-jitar da ke cewa ADC ba za ta fitar da ‘yan takara a zaɓen 2027 ba. Muna ganin irin waɗannan maganganu a matsayin marasa tushe, na yaudara, kuma an yi su ne domin haddasa ruɗani ba tare da wani dalili ba.”

Jam’iyyar ta sake jaddada cewa babu wani cikas na doka da zai hana ta shiga zaɓen 2027, tana mai cewa tana bin dukkan tanade-tanaden kundin tsarin mulki da dokar zaɓe.

“Mu fayyace: ADC za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen 2027—‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma masu karɓuwa a faɗin ƙasa waɗanda za su iya jagorantar ƙasar nan daga halin da take ciki,” in ji sanarwar.

Jam’iyyar ta kuma bayyana kanta a matsayin babbar jam’iyyar adawa, tana mai mai da hankali kan haɗa kan ‘yan Nijeriya da gina tsari mai ƙarfi domin samun nasara a zaɓe.

“Ba mu damu da surutu ba. Muna mai da hankali kan ainihin aiki—shirya jama’a a faɗin ƙasa, jawo hankalin ‘yan Nijeriya da suka gaji da rashin tsaro, tsadar rayuwa, da ƙarancin damar rayuwa, tare da gina tsarin da ba wai kawai zai ba mu damar tsayawa takara ba, har ma da cin zaɓe,” in ji jam’iyyar.

ADC ta buƙaci mambobinta, magoya bayanta, da sauran jama’a da su yi watsi da abin da ta kira jita-jita marasa tushe, tana mai cewa aikin da ke gaba na buƙatar haɗin kai da jajircewa, ba zato-zato ba.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Next Post
MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.