ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Gabatar Da ‘Yan Takara A Kowacce Kujera A Zaɓen 2027 — ADC

by Muhammad
1 month ago

Jam’iyyar ADC ta bayyana cewa za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen duk gari na 2027, tana mai watsi da jita-jitar da ke cewa ba za ta shiga zaɓen ba, inda ta bayyana zantukan a matsayin marasa tushe.

Jam’iyyar ta ce duk da abin da ta kira “sabbin rikice-rikice,” tana nan daram kan burinta na ceto Nijeriya daga abin da ta bayyana a matsayin rashin kyakkyawan shugabanci na jam’iyyar APC, tare da hana ƙasar fadawa tsarin jam’iyya ɗaya.

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, ADC ta bayyana rahotannin da ke cewa ba za ta gabatar da ‘yan takara ba a 2027 a matsayin “marasa tushe ba tare da hujja ba.”

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta jaddada cewa a shirye take tsaf domin shiga zaɓen, tana mai cewa tana aiki tukuru domin gabatar da ‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma waɗanda za su samu karɓuwa a matakin ƙasa baki ɗaya.

Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar ADC na so ta bayyana a sarari cewa muna nan kan ƙudurinmu na ceto Nijeriya daga gazawar gwamnatin APC da kuma hana ƙasar shiga tsarin jam’iyya ɗaya mai haɗari.”

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

Ta ƙara da cewa: “Mun lura da jita-jitar da ke cewa ADC ba za ta fitar da ‘yan takara a zaɓen 2027 ba. Muna ganin irin waɗannan maganganu a matsayin marasa tushe, na yaudara, kuma an yi su ne domin haddasa ruɗani ba tare da wani dalili ba.”

Jam’iyyar ta sake jaddada cewa babu wani cikas na doka da zai hana ta shiga zaɓen 2027, tana mai cewa tana bin dukkan tanade-tanaden kundin tsarin mulki da dokar zaɓe.

“Mu fayyace: ADC za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen 2027—‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma masu karɓuwa a faɗin ƙasa waɗanda za su iya jagorantar ƙasar nan daga halin da take ciki,” in ji sanarwar.

Jam’iyyar ta kuma bayyana kanta a matsayin babbar jam’iyyar adawa, tana mai mai da hankali kan haɗa kan ‘yan Nijeriya da gina tsari mai ƙarfi domin samun nasara a zaɓe.

“Ba mu damu da surutu ba. Muna mai da hankali kan ainihin aiki—shirya jama’a a faɗin ƙasa, jawo hankalin ‘yan Nijeriya da suka gaji da rashin tsaro, tsadar rayuwa, da ƙarancin damar rayuwa, tare da gina tsarin da ba wai kawai zai ba mu damar tsayawa takara ba, har ma da cin zaɓe,” in ji jam’iyyar.

ADC ta buƙaci mambobinta, magoya bayanta, da sauran jama’a da su yi watsi da abin da ta kira jita-jita marasa tushe, tana mai cewa aikin da ke gaba na buƙatar haɗin kai da jajircewa, ba zato-zato ba.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.