ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Gabatar Da ‘Yan Takara A Kowacce Kujera A Zaɓen 2027 — ADC

by Muhammad
2 months ago

Jam’iyyar ADC ta bayyana cewa za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen duk gari na 2027, tana mai watsi da jita-jitar da ke cewa ba za ta shiga zaɓen ba, inda ta bayyana zantukan a matsayin marasa tushe.

Jam’iyyar ta ce duk da abin da ta kira “sabbin rikice-rikice,” tana nan daram kan burinta na ceto Nijeriya daga abin da ta bayyana a matsayin rashin kyakkyawan shugabanci na jam’iyyar APC, tare da hana ƙasar fadawa tsarin jam’iyya ɗaya.

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar a ranar Asabar, ADC ta bayyana rahotannin da ke cewa ba za ta gabatar da ‘yan takara ba a 2027 a matsayin “marasa tushe ba tare da hujja ba.”

ADVERTISEMENT

Jam’iyyar ta jaddada cewa a shirye take tsaf domin shiga zaɓen, tana mai cewa tana aiki tukuru domin gabatar da ‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma waɗanda za su samu karɓuwa a matakin ƙasa baki ɗaya.

Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar ADC na so ta bayyana a sarari cewa muna nan kan ƙudurinmu na ceto Nijeriya daga gazawar gwamnatin APC da kuma hana ƙasar shiga tsarin jam’iyya ɗaya mai haɗari.”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Ta ƙara da cewa: “Mun lura da jita-jitar da ke cewa ADC ba za ta fitar da ‘yan takara a zaɓen 2027 ba. Muna ganin irin waɗannan maganganu a matsayin marasa tushe, na yaudara, kuma an yi su ne domin haddasa ruɗani ba tare da wani dalili ba.”

Jam’iyyar ta sake jaddada cewa babu wani cikas na doka da zai hana ta shiga zaɓen 2027, tana mai cewa tana bin dukkan tanade-tanaden kundin tsarin mulki da dokar zaɓe.

“Mu fayyace: ADC za ta gabatar da ‘yan takara a zaɓen 2027—‘yan takara nagari, ƙwararru, kuma masu karɓuwa a faɗin ƙasa waɗanda za su iya jagorantar ƙasar nan daga halin da take ciki,” in ji sanarwar.

Jam’iyyar ta kuma bayyana kanta a matsayin babbar jam’iyyar adawa, tana mai mai da hankali kan haɗa kan ‘yan Nijeriya da gina tsari mai ƙarfi domin samun nasara a zaɓe.

“Ba mu damu da surutu ba. Muna mai da hankali kan ainihin aiki—shirya jama’a a faɗin ƙasa, jawo hankalin ‘yan Nijeriya da suka gaji da rashin tsaro, tsadar rayuwa, da ƙarancin damar rayuwa, tare da gina tsarin da ba wai kawai zai ba mu damar tsayawa takara ba, har ma da cin zaɓe,” in ji jam’iyyar.

ADC ta buƙaci mambobinta, magoya bayanta, da sauran jama’a da su yi watsi da abin da ta kira jita-jita marasa tushe, tana mai cewa aikin da ke gaba na buƙatar haɗin kai da jajircewa, ba zato-zato ba.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

MURIC Ta Zargi Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Da Fifita Kiristoci Fiye Da Musulmi

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.