Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona na dab da kammala ɗaukar ɗan wasan gaban Arsenal, Gabriel Jesus, kan yarjejeniyar da aka ruwaito ta kai fam miliyan 8.6. Ana kyautata zaton cewa cinikin ya kusa kammala, inda ake sa ran ɗan wasan na Brazil zai rattaba hannu kan yarjejeniyar ƙashin kansa kafin rufe kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa gobe Talata.
Rahotanni sun ce Jesus, mai shekaru 29, zai yi gwajin lafiya a birnin Barcelona a yau Litinin kafin kammala cinikin. Tsohon ɗan wasan Manchester City ya samu tayin komawa Napoli, amma ya zaɓi komawa Barcelona domin ci gaba da buga gasar La Liga.
Jesus ya koma Arsenal a shekarar 2022, inda ya zura kwallaye 32 tare da taimakawa wajen jefa wasu 22 a wasanni 123 da ya buga wa ƙungiyar. Kocin Arsenal, Mikel Arteta, ya tabbatar a ranar Alhamis cewa ɗan wasan bai halarci atisayen ƙungiyar ba yayin da ake shirin karawa da Aston Villa a gasar Premier League.
Da aka tambayi Arteta ko rashin halartar atisayen na da alaƙa da yiwuwar barin ƙungiyar, kocin ya ce: “Wannan abu ne da ya shafi Jesus.” Wannan martani ya ƙara ƙarfafa rahotannin da ke cewa ɗan wasan na shirin barin Emirates.
Idan cinikin ya kammala, Gabriel Jesus zai zama ɗaya daga cikin sabbin ‘yan wasan da Barcelona ta dauka daga ƙungiyoyin Premier League a wannan bazarar, bayan Anthony Gordon daga Newcastle United da Rodri daga Manchester City.














