Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, a matsayin wanda ke yawan tsayawa takara amma yana shan kaye, yana mai cewa da alama zai sake tsayawa takara a shekarar 2031. Wike ya faɗi haka ne a wani martani ga kalaman Atiku da ya zargi gwamnatin da ke mulki da cewa ba ta yi wani abin kirki ga ‘yan Nijeriya ba.
Yayin da yake duba ayyukan titunan da ke gudana a Abuja, ministan ya ce ‘yan Nijeriya ba za su ɗauki irin wannan suka da muhimmanci ba, yana mai nuni da irin ci gaban da ake gani a faɗin FCT a matsayin hujja. Ya ƙara da cewa Atiku ya kamata ya kwatanta halin da Abuja take ciki yanzu da lokacin da yake mataimakin shugaban kasa, yana tambayar ko za a iya cewa daidai suke.
INEC Ta Amince Da Shugabancin PDP Tsagin Wike
Ba Zan Goyi Bayan Tinubu A 2027 Kamar Wike Ba — Makinde
Wike ya jaddada cewa gwamnati ba za ta bari kalaman siyasa su ɗauke hankalinta daga aiki ba, yana mai cewa dole ne a ci gaba da gudanar da ayyuka duk da batun zabe. Ya kuma tabbatar da cewa muhimman ayyukan tituna da ke haɗa garuruwan wajen birni za su kammala a kan lokaci domin inganta zirga-zirga da rage cunkoso a tsakiyar birnin.
Ya bayyana cewa aikin titin Filin Jirgin Sama zuwa Kuje na gab da kammaluwa, inda wani ɓangare na gadar zai fara aiki mako mai zuwa, yayin da ake sa ran kammala gaba ɗaya aikin kafin ƙarshen watan Mayu. Haka kuma, ya ce zangon farko na aikin faɗaɗa titin Kuje zuwa Gwagwalada mai tsawon kusan kilomita bakwai zai kammala kafin ƙarshen watan Mayu, yana mai nuna gamsuwa da ingancin aikin.
Ministan ya ƙara da cewa waɗannan ayyuka za su sauya Kuje zuwa wata muhimmiyar cibiyar zama da kasuwanci, inda mutane za su koma can su gina gidaje, lamarin da zai rage cunkoso a cikin birnin Abuja.














Discussion about this post