ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
Mata

An kusa fara Gasar Cin Kofin Afirka ta Mata (WAFCON), inda Morocco za ta karbi bakunci karo na biyu a jere. Za a fara buga wasannin ne daga ranar Asabar 5 ga watan Yuli, inda mai masaukin baki, Morocco za ta fafata da Zambiya a filin wasa na Olympic a birnin Rabat. Kasar da ta lashe kofin karo tara a tarihi, Nijeriya tana cikin wasannin, wadda za ta fara kece raini da Tunisia a rukuni na biyu a makon farko sai kuma rike da kofin, Afirka ta Kudu za ta kara da Ghana a wasan farko a rukuni na uku ranar Litinin 7 ga Yuli.

An raba tawagar 12 zuwa rukuni uku, inda kowane rukuni ke dauke da tawaga hudu. Mai masaukin baki Morocco tana da jan aiki a gabanta a rukunin farko, an kuma hada ta da Zambiya, wadda ta doke a wasannin neman shiga Olympic 2024. Haka kuma Morocco za ta fuskanci Senegal da Jamhuriyar Congo, inda biyu ne za su kai zagaye na biyu a gasar.

  • Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali
  • Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Tawagar Nijeriya na fatan sake lashe kofin, wanda rabonta da shi tun 2018, kuma ita ce kan gaba wajen iya kwallo a Afirka sannan ta 36 a duniya. Tawagar Nijeriya ta Super Falcons za ta kece raini a rukuni na biyu da ya kunshi Tunisia da Algeria da kuma Botswana.

ADVERTISEMENT

Rukuni na uku kuwa ya hada da mai rike da kofin, Afirka ta Kudu, wadda za ta fara fuskantar Ghana, sai kuma Mali, wadanda za su yi wasannin a karo tun bayan 2018 da kuma Tanzania, wadda za ta buga gasar a karo na

biyu tun bayan 2010. Duk kungiya biyu da ta hada maki da yawa za ta kai zagayen gaba a kowanne rukuni da kuma biyu da suka sami maki mai yawa, amma suka kara a mataki na uku a cikin rukuni.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

 

Rukunin farko: Morocco da Zambiya da Senegal da kuma Jamhuriyar Congo

Rukuni na biyu: Nijeriya da Tunisia da Algeria da kuma Botswana.

Rukuni na uku: Afirka ta Kudu da Ghana da Mali da kuma Tanzania.

Bayan karawar bude labulen gasar, akalla za a rika buga wasanni bibiyu kowacce rana a fafatawar cikin rukuni har zuwa ranar Litinin 14 ga watan Yuli. Sannan a lokacin wasannin cikin rukuni za ake buga su daga 13:00 da 16:00 da kuma19:00 daidai da agogon GMT. Za a fara karawar zagaye na biyu daga ranar Juma’a 18 ga watan Yuli.

Shekara ukun da ta gabata, Morocco ta gudanar da gasar cin kofin Afirka ta mata, kuma filaye ukun da ta yi amfani da su, ba bu su daga cikin wadanda za su karbi bakuncin gasar bana. Kasar dake Arewacin Afirka na ci gaba da yin tsare-tsare da gyare-gyare, wadda za ta karbi bakuncin wasan cin kofin Afirka na maza da yin hadakar gasar cin kofin duniya da za a buga a 2030.

 

Za A Yi Amfani Da Filayen Wasa Shida A Birane Biyar Har Da Biyu A

Casablanca:

Olympic Stadium a Birnin Rabat (Mai cin ‘yan kallo 21,000)

El Bachir Stadium a Birnin Mohammedia (Mai cin ‘yan kallo 15,000)

Larbi Zaouli Stadium a Birnin Casablanca (Mai cin ‘yan kallo 30,000)

Pere Jego Stadium a Birnin Casablanca (Mai cin ‘yan kallo 10,000)

Honneur Stadium a Birnin Oujda (Mai cin ‘yan kallo 19,800)

Berkane Stadium a Birnin Berkane (Mai cin ‘yan kallo 15,000

Daga kasashe 12 da za su buga gasar cin kofin Afirka a Morocco, NIjeriya ce da Afirka ta Kudu ta taba daukar kofin. Super Falcons za ta fafata a wasannin karkashin koci, Justin Maduguwu. Chiamaka Nnadozie daga NIjeriya ita ce ta lashe kyautar fitatciyar mai tsaron raga a Afirka karo biyu, yayin da Asisat Oshoala za ta buga wasannin da ta dunga yin fice a baya.

Mai horar wa Desiree Ellis za ta yi kokarin kare kofin da yake hannun Afirka ta kudu, wadda za ta buga karawar ba tare da Thembi Kgatlana, saboda wasu dalilai na kashin kai. Haka ‘yar wasan Afirka ta Kudu, Jermaine Seoposenwe tana taka rawar gani a Monterrey a Medico da Hilda Magaia, wadanda aka rabawa takalmin zinare a matakin kan gaba a cin kwallaye a WAFCON a 2022.

Morocco tana zuba hannun jari mai yawa a fannin kwallon kafa a ‘yan shekaru da yawa, amma har yanzu tawagarta ta mata ta kasa kwaikwayon ta maza da ta taba taka matakin farko a buga wasa a Afirka. Sai dai Atlas Lionesses tana da mai horar wa Jorge Bilda, wanda ya lashe kofin duniya da tawagar Sifaniya a 2023. Zambia ta kare a mataki na uku a gasar baya da aka yi, tana kuma tare da wadda ta yi fice a fannin buga

mata wasa a Afirka a shekara, Barbra Banda, wadda ba ta buga gasar 2022 ba.

Mai buga wasa a Orlando Pride tana kan ganiya, wadda take wasa tare da Racheal Kundananji, wadanda suna daga cikin ‘yan wasa hudun da aka saya mafi tsada a tarihi. Ita kuwa ‘yar kasar Swistzerland, Nora Hauptel za ta ja ragamar Ghana ne domin lashe gasar karon farko a tarihi.

Bayan Nijeriya da Afirka ta Kudu da suke da tarihin lashe gasar kofin Afirka, Ghana tana da kwarewar halartar wasannin da ta yi a 1998 da 2002 da kuma 2006.

 

Wasannin cikin rukuni

Asabar 5 ga watan Yuli

Rukunin farko: Morocco da Zambia – Ranar Lahadi 6 ga watan Yuli

Rukunin farko: Senegal da Ibory Coast, El Bachir Stadium, Mohammedia

(14:00)

Rukunin na biyu: Nijeriya da Tunisia, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (16:00)

Rukunin na biyu: Algeria bs Botswana, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)

 

Ranar Litinin 7 ga watan Yuli

Rukunin na uku: Afirka ta Kudu da Ghana, Honneur Stadium, Oujda

(16:00)

 

Rukunin na uku: Mali da Tanzania, Berkane Stadium, Berkane (19:00)

Ranar Laraba 9 ga watan Yuli

Rukunin farko: Zambiya da Senegal, Mohammedia (16:00)

Rukunin farko: Jamhuriyar Congo da Morocco, Rabat (19:00)

 

Ranar Alhamis 10 ga watan Yuli

Rukunin na biyu: Botswana da Nijeriya, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (16:00)

Rukunin na biyu: Tunisia da Algeria, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)

Ranar Juma’a 11 ga watan Yuli

Rukunin na uku: Ghana da Mali, Berkane (16:00)

Rukunin na uku: Tanzania da South Africa, Oujda (19:00)

Ranar Asabar 12 ga watan Yuli

Rukunin farko: Morocco da Senegal, Rabat (19:00)

Rukunin farko: Zambiya da Jamhuriyar Congo, Mohammedia (19:00)

 

Ranar Lahadi 13 ga watan Yuli

Rukunin na biyu: Nijeriya da Algeria, Larbi Zaouli Stadium, Casablanca (19:00)

Rukunin na biyu: Tunisia da Botswana, Pere Jego Stadium, Casablanca (19:00)

Ranar Litinin 14 ga watan Yuli

Rukunin na uku: Afirka ta Kudu da Mali, Oujda (19:00)

Rukunin na uku: Ghana da Tanzania, Berkane (19:00)

Zagayen kwata fainal a WAFCON 2024

 

Ranar Juma’a 18 ga watan Yuli

Kwata fainal na farko: Wadda ta yi ta daya a rukunin farko da ta farko a rukuni na uku ko wadda ta yi ta uku a rukuni na biyu, za su yi wasa a Rabat

Kwata fainal na biyu: Wadda ta yi ta farko a rukuni na biyu da wadda ta yi ta biyu a rukunin farko, za su kece raini a Larbi Zaouli Stadium a Casablanca.

 

Ranar Asabar 19 ga watan yuli

Kwata fainal na uku: Wadda ta yi ta farko a rukuni na uku da ta daya a rukunin farko ko wadda ta kare a mataki na uku a rukuni na biyu, za su kara a Oujda

Kwata fainal na hudu: Wadda ta yi ta biyu a rukuni na biyu da wadda ta kare a mataki na biyu a rukuni na uku, za su yi wasa a Berkane

 

Wasannin dab da karshe a WAFCON 2024

Wasan dab da karshe na farko: Wadda ta ci zagayen kwata fainal a wasan farko za ta fuskanci wadda ta yi nasara a zagayen kwata final karawa ta hudu, za su kara a birnin Rabat.

Wasan dab da karshe na biyu: Wadda ta lashe zagayen kwata fainal wasa na biyu da wadda ta yi nasara a karawar kwata fainal na uku, za su kece raini a Larbi Zaouli Stadium a Casablanca.

Wasan neman mataki na uku da na hudu

Ranar Juma’a 25 ga watan Yuli

Wadda ta yi rashin nasara a dab da karshen farko da wadda aka doke a zagayen dab da karshe wasa na biyu, za su fafata a Larbi Zaouli Stadium a birnin Casablanca.

Wasan karshe na WAFCON 2024

Ranar Asabar 26 ga watan Yuli

Wadda ta lashe wasan farko na dab da karshe da wadda ta yi nasara a dab

da karshe na biyu, inda za su fafata a Olympic Stadium a Birnin Rabat.

Mata
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.