Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya dakatar da ɗaya daga cikin masu kula da shafinsa na Facebook saboda wani rubutu mai tayar da ƙura da aka wallafa kan wasu mutane da malamai da ba sa goyon bayan burinsa na tsayawa takarar gwamnan Jihar Gombe.
Pantami, wanda ke shirin tsayawa takarar gwamnan Jihar Gombe a ƙarƙashin jam’iyyar APC, ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Asabar.
Tsohon ministan ya nesanta kansa da rubutun, yana mai cewa ba da izininsa aka wallafa shi ba kuma ya saɓa da ƙa’idojin jagorancinsa.
“Hankalina ya kai ga wani rubutu da ɗaya daga cikin masu kula da wannan shafi ya wallafa, wanda ke ɗauke da saƙo mai tsauri da ke nuna cewa duk wanda bai goyi bayan Farfesa Pantami ba munafiki ne, haka kuma duk malamin da bai mara masa baya ba shi ma munafiki ne,” in ji shi.















Discussion about this post