ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gudunmawar Likitocin Dabbobi Wajen Hana Barkewar Cututtuka

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
1 month ago
Likitocin

Ranar Likitocin Dabbobi Ta Duniya muhimmiyar rana ce da aka ware domin bitar rawar da likitocin dabbobi ke takawa wajen kare lafiyar dabbobi, tsaron abinci da lafiyar jama’a.

A na gudanar da bukin muhimmiyar ranar ne a kowace shekara a ranar Asabar din karshe ta watan Afrilu domin wayar da kan al’umma kan muhimmancin fannin likitocin dabbobi a rayuwar yau da kullum. Taken taron na bana shine Likitocin Dabbobi: Ginshikin Kare Abinci Da Lafiya.

Ranar 25 ga Afrilu din makon jiya da aka gudanar da bukin zagayowar ranar ta 2026, an gudanar da muhimman taruka da bita tare da jaddada gudunmuwar da likitocin dabbobi ke bayarwa wajen hana yaduwar cututtuka, kula da dabbobi da kuma tabbatar da ingantaccen abinci ga al’umma wadda dama ce ga kasashe da kungiyoyi domin kara karfafa manufofi da zuba jari a fannin domin inganta tsaron lafiya da abinci a fadin duniya.

ADVERTISEMENT

Yayin da duniya ke bukin tunawa da ranar likitocin dabbobi, kungiyar likitocin dabbobi a Nijeriya ta jaddada cewar wannan lokaci bai kamata ya tsaya ga shagulgula kawai ba, kamata ya yi ya zama matakin kawo sauyi mai ma’ana wajen daukar matakan da za su bunkasa fannin a tsarin manufofin kasa

A bayyane yake cewar gudunmuwar da likitocin dabbobi ke bayarwa wajen kare lafiyar al’umma ta hanyar kula da lafiyar dabbobi da hana yaduwar cututtuka musamman daga mahauta ta fi gaban a nanata; hasalima tuni fannin ya zama kinshiki mai zaman kansa wajen tabbatar da tsaron abinci da lafiyar jama’a.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Kima da tasirin likitocin dabbobi muhimmi ne domin kuwa lafiyar dabbobi da ta mutane suna da alaka kai tsaye ta kut da kut ta yadda kai tsaye za a iya cewa cututtuka da dama na wucewa daga dabbobi zuwa mutane wanda hakan ke nuna kula da lafiyar dabbobi na nufin kare lafiyar dan Adam.

Likitocin dabbobi na da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen gano cututtuka da wuri, gudanar da allurar rigakafi da kuma sa idanu kan lafiyar dabbobi domin hana barkewar annoba a cikin al’umma.

A yayin da duniya ke bukin muhimmiyar ranar, kwararrun likitocin dabbobi a Nijeriya sun yi kakkausan gargada cewar tsarin tsaron abinci, lafiyar jama’a da kuma kare muhalli na kasar na fuskantar babbar barazana kamar yadda shugaban kungiyar na kasa, Dakta Moses Arokoyo ya bayyana a ranar.

A kan wannan kungiyar ta bukaci daukar kwararan matakan gaggawa wajen inganta fannin, kara zuba jari da kuma baiwa likitocin dabbobi kulawa tare da bayyana shi a matsayin fannin da ke da matukar tasiri ga rayuwar al’umma.

Kungiyar ta bayyana cewar, kula da lafiyar jama’a da kuma daidaiton muhalli na fuskantar karin barazana sakamakon karancin kudi, raunin da ke akwai a tsarin hukumomi da kuma gazawar aiwatar da manufofi yadda ya kamata.

Shugaban kungiyar, Arokoyo ya bayyana cewa halin da ake ciki ya kai wani matsayi mai hatsari sakamakon sakaci, raunin aiwatar da manufofii da kuma karancin zuba jari a fannin kiwon lafiyar dabbobi.

A cewarsa, Nijeriya ba za ta iya ci- gaba da daukar sha’anin likitancin dabbobi a matsayin karamin abu ba a cikin tsarin tsara manufofin kasa ba, ya jaddada cewa fannin na da matukar muhimmanci domin yana taka muhimmiyar rawa kai tsaye wajen tabbatar da rayuwar al’umma, ingancin abinci da kuma lafiyar jama’a.

A kan wannan kungiyar ta bukaci gwamnati da hukumomin da lamarin ya shafa su dauki matakan gaggawa ciki har da kara zuba jari, inganta tsarin kula da lafiyar dabbobi da kuma karfafa dokoki da manufofi domin magance barazanar da ke kara kamari.

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewar masanan sun kuma bayyana cewar idan aka samu hadin guiwa a tsakanin sassan lafiya, noma da muhalli za su taimaka sosai wajen rage hadarin cututtuka da tabbatar da ingantaccen abinci ga al’umma.

A wani kakkausan gargadi, shugaban kungiyar Dakta Arokoyo ya bayyana likitocin dabbobi a matsayin wani ginshikin bayan fage a tsarin abinci a Nijeriya wanda ke sahun gaba wajen kare cututtukan da ke wucewa a boye tsakanin dabbobi da mutane.

Shugaban ya yi gargabin cewa duk da yadda aka fi mayar da hankali kan asibitoci da magungunan mutane, ainihin inda ake fara yaki da cututtuka shi ne a gonaki, mahauta, kasuwannin dabbobi da kuma dakunan gwaje-gwaje a inda lafiyar dabbobi ke tantance lafiyar mutane tun kafin barkewar cuta ta kai garuruwa.

“Daga gonaki, mahauta, zuwa teburin abinci, daga dakin gwaje-gwaje zuwa tsara dokoki, likitancin dabbobi ne ke dora ginshkiin tsaron abinci da lafiyar kasa wanda a kan hakan kadai ya kamata a ce fannin ya samu kulawar musamman.”

Haka ma kungiyar ta kuma nuna damuwa kan gazawar gwamnatin kasar nan wajen bai wa fannin isassun kudi da kulawar da ta kamata wanda rashin yin hakan ke haifar da babban gibi mai hadari wajen dakile cututtuka kafin su barke a cikin al’umma.

Kungiyar ta bayyana cewa yanzu haka Nijeriya na fuskantar haduwar babbar barazanar da ta hada da sauyin yanayi, juriyar magunguna da kuma bullar sabbin cututtukan da ke wucewa daga dabbobi zuwa mutane wadanda matsalolin na kara nuna yadda lafiyar dabbobi, ta mutane da kuma muhalli suke da alaka ta kusa- kusa.

A cewar shugaban kungiyar, duniya ta riga ta shiga wani zamani na matakin “Lafiya Daya” ta yadda barkewar cututtuka ba su bin iyakokin da aka saba da su a baya. Ya ce a yanzu cututtuka suna yaduwa cikin sauri tsakanin dabbobi da mutane, yayin da matsin lambar muhalli ke kara hanzarta yaduwarsu.

A kan wannan shugaban ya bayyana cewar rawar da likitocin dabbobi ke takawa na kara zama gagaruma musamman wajen gano barkewar cututtuka da wuri, gudanar da allurar rigakafi, duba ingancin abinci da dakile yaduwar annoba.

Ya ce ko kadan ba za a iya raba lafiyar dan Adam da ta dabba ko muhalli ba, don haka ya zama wajibi a dauki matakan da suka kamata na hadin guiwa domin kare rayuwar al’umma.

Duk da wannan karin nauyi da ake dorawa likitocin dabbobi, kungiyar a Nijeriya ta nuna damuwa kan yadda har yanzu ake raina fannin, ba a ba shi isassun kudi kuma ba a baiwa fannin kulawa a yayin tsara manufofiin kasa.

Haka ma kungiyar ba ta yi kasa a guiwa ba wajen bayyana cewar daya daga cikin manyan matsalolin da aka fi mayar da hankali a kai shi ne rashin ingantaccen bayanai kan dabbobi da lafiyarsu a Nijeriya wanda babban gibi ne da kungiyar ta ce yana hana ingantaccen tsarin tattalin arziki da kuma dakile cututtuka yadda ya kamata.

A kan wannan shugaban kungiyar Dakta, Arokoyo ya yi kira da a gaggauta gudanar da shirin kidayar dabbobi na kasa yana mai gargadin cewar idan babu cikakkun bayanai, a na daukar kwararan matakai ne a cikin duhu kawai.

A kan wannan kungiyar ta jaddada muhimmancin tattara sahihan bayanai domin a cewar ta idan ba a yi gwajin abu ba to tamkar bai wanzu ba ne a tsarin manufofi don haka gwajin ke da tasirin gaske.

Haka ma kungiyar ta ce bayanai kan allurar rigakafi, matakan da ake dauka a yayin  barkewar cututtuka da kuma sakamakon binciken nama, duka ba a rubuta su yadda ya kamata wanda hakan ke hana jawo hankalin masu zuba jari ko kawo gyara mai ma’ana a wannan fannin.

Kungiyar ta kuma fallasa amfani da magungunan dabbobi da ake yi ba bisa ka’ida ba tare da gargadin cewa wannan na iya kara saurin yaduwar matsalar juriyar magunguna wadda barazana ce ta duniya da ke iya sa cututtukan yau da kullum su zama ba su yin magani ga dabbobi da mutane lamarin da shugaban kungiyar ya bayyana cewar ba matsalar likitocin dabbobi ba ce kadai matsalar ceton rayuwa ce bakidaya.

Sai dai duk da muhimmancin da fannin ke da shi bincike ya nuna har yanzu a na fama da sakaci a tsarin don haka akwai bukatar aiwatar da cikakken tsarin likitocin dabbobi na kasa wanda zai shawo kan kara yawan ma’aikata a matakan jihohi da kananan hukumomi da tabbatar da isassun kudi ga shirye-shiryen allurar rigakafi, gyaran mahauta da kuma tsarin sa ido kan cututtuka.

A kan wannan za a iya cewar rashin daukar matakai zai kara jefa al’ummar kasa a cikin hadarin barkewar cututtuka da za a iya kaucewa, karancin abinci da kuma asarar tattalin arziki mai yawa a fannin kiwon dabbobi wanda daya ne daga cikin manyan ginshikan noma da kiyo.

A kan wannan za a ga cewar ci-gaba da yin sakaci da tsarin kiwon lafiyar dabbobi ba karamin kuskure ba ne domin babbar barazana ce ga rayuwar kasa da tsaronta don haka ya zama wajibi a bayar da kulawar da ta kamata.

Kwararrun likitocin dabbobi na taka muhimmiyar rawa a dukkan matakan samar da abinci tun daga kan kiwon dabbobi da rigakafin cututtuka zuwa duba mahauta, bincike a dakunan gwaje-gwaje da sa ido kan cututtuka har zuwa ba da shawara wajen tsara manufofi.

A kan gudunmuwar likitocin dabbobi wajen tabbatar da yanka lafiyayyun dabbobi a mahauta, kwararrun likitocin sun jaddada muhimmiyar rawar da suke takawa wajen kare barkewar cututtuka, musamman ta hanyar tabbatar da lafiyar dabbobin da ake amfani da su wajen samar da abinci.

A cewar shugagaban kungiyar, Dakta Arokoyo, likitocin dabbobi su ne sahun gaba wajen hana yaduwar cututtuka, musamman wadanda ke wucewa daga dabbabi zuwa mutane, ya ce matakan kariya na farawa ne tun daga gonaki, kasuwannin dabbobi da kuma mahauta a inda lafiyar dabbobi ke da tasiri kai tsaye ga lafiyar mutane kafin cuta ta kai ga al’umma.

Rahotanni sun tabbatar da cewar likitocin dabbobi na bayar da gagarumar gudunmuwa daga kan kiwon dabbobi, rigakafin cututtuka, zuwa duba lafiyar nama a mahauta da kuma bincike a dakunan gwaje-gwaje wanda a bayyane tsarin na taimakawa wajen tabbatar da ganin abincin da ake ci ba ya dauke da cututtuka tare da rage yiwuwar barkewar annoba.

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewar a mahauta, aikin likitocin dabbobi yana da matukar muhimmanci wajen tabbatar da  lafiyayyun dabbobi kawai ake yankawa, hasalima masana sun bayyana cewa rashin kula da tsafta da kuma rashin sa idon  kwararru a irin wadannan wurare na iya janyo yaduwar cututtukan da ake samu daga abinci wanda ke barazana ga lafiyar jama’a.

Sai dai duk da wannan muhimmanci, kungiyar likitocin dabbobi ta yi gargadi kan yawaitar ma’aikatan bogi da ke amfani da magungunan dabbobi ba bisa ka’ida ba wanda babbar matsala ce mai zaman kan ta da suke fatar ganin an shawo kan ta da ke kara tsanantar matsalar juriyar magunguna da ke barazana ga lafiyar dabbobi da mutane.

A bayyane yake cewar likitocin dabbobi na bayar da gagarumar gudunmuwa a rayuwar al’umma, hasalima su ne ginshikin tabbatar da kariyar abinci da hana yaduwar cututtuka musamman a yanayin gurbacewar sha’anin kiyon lafiya a duniya da ke kara tsananta.

Likitocin
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Tashoshin Ruwan Nijeriya Za Su Yi Daidai Da Na Manyan Kasashen Duniya – Dantsoho

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.