ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashoshin Ruwan Nijeriya Za Su Yi Daidai Da Na Manyan Kasashen Duniya – Dantsoho

by Bello Hamza
2 months ago
Tashoshin

Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Zartarwa na Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA), Dakta Abubakar Dantsoho, ya ce da sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa, tsarin tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya zai shiga sabon mataki tare da zama jagora a harkar sufurin ruwa a nahiyar Afirka.

Dantsoho ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron Zuba Jari na Tattalin Arzikin Teku (Blue Economy Inbestment Summit) da aka gudanar a Abuja, inda ya ce tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya za su taka muhimmiyar rawa wajen jawo manyan masu zuba jari da kuma hanzarta bunkasar tattalin arziki.

Sai dai ya danganta sauyin da ake samu a bangaren harkar ruwa da tasirin Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Teku, Dakta Adegboyega Oyetola, da kuma sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa.

ADVERTISEMENT

Ya kuma tabbatar wa masu zuba jari cewa Nijeriya na da karfin zama jagora a tattalin arzikin tekun Afirka (blue economy), yana mai cewa gyare-gyaren gwamnati da kuma karuwar shigar masu zaman kansu su ne manyan ginshikan wannan sauyi.

Ya ce dole ne Nijeriya ta mayar da hankali wajen amfani da albarkatun tekunta yadda ya kamata domin cimma manufofin ci gaban duniya mai dorewa.

LABARAI MASU NASABA

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

“Lokaci ya yi da za a sauya tsarin tattalin arzikin Nijeriya zuwa yadda za a yi cikakken amfani da albarkatun tekunmu. Idan aka yi amfani da tsarin tashoshin jiragen ruwa yadda ya kamata, zai iya zama babban ginshiki na bunkasar tattalin arziki,” in ji shi.

Shugaban NPA ya bayyana cewa matsayi na Nijeriya a taswirar duniya, yawan al’umma da karfin tattalin arziki suna ba ta damar zama cibiyar harkar ruwa a Yammacin Afirka, kamar kasashe irin su Singapore da Morocco.

“Saboda matsayinta na dabaru, girman kasuwa da karfin tattalin arziki, Nijeriya na da damar zama cibiyar harkar jiragen ruwa ta Yammacin Afirka,” in ji shi.

Duk da wadannan damar, Dantsoho ya nuna damuwa cewa a halin yanzu Nijeriya na sarrafa kusan kashi 25 cikin 100 ne kawai na zirga-zirgar kaya a yankin, duk da cewa tana dauke da fiye da kashi 60 cikin 100 na GDP na Yammacin Afirka.

“Abin damuwa ne cewa Nijeriya, duk da cewa tana da sama da kashi 60 cikin 100 na GDP na Yammacin Afirka, tana sarrafa kusan kashi 25 cikin 100 ne kawai na jigilar kaya a yankin. Wannan a fili yana nuna cewa ba mu yi amfani da cikakken damar da muke da ita ba,” in ji shi.

Dantsoho ya jaddada cewa gasa a harkar sufurin ruwa ta duniya na bukatar ingantaccen aiki, farashi mai gasa da kuma kyakkyawar hadin kai tsakanin yankunan cikin kasa da tashoshin ruwa, yana mai cewa dole ne tashoshin Nijeriya su ci gaba da sabawa da sauye-sauyen da ke faruwa a harkar sufurin ruwa a duniya.

“Idan aka ci gaba da aiwatar da wadannan tsare-tsare yadda ya kamata, tsarin tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya zai shiga sabon mataki tare da zama jagora a harkar sufurin ruwa a Afirka,” in ji shi.

Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Teku, Adegboyega Oyetola, a jawabinsa na farko, ya ce albarkatun da Nijeriya ke da su, ciki har da bakin tekun ta mai tsawon kilomita 823 da manyan hanyoyin ruwa na cikin kasa, suna ba ta damar jagorantar wannan bangare.

“Da bakin teku mai tsawon kilomita 823, manyan hanyoyin ruwa na cikin kasa da kuma matsayi mai muhimmanci a Tekun Guinea, Nijeriya na da damar musamman wajen amfani da albarkatun tattalin arzikin ruwa,” in ji Oyetola.

Ya kara da cewa sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke yi sun inganta hadin kai, karfafa tsaron teku da kuma kara amincewar masu zuba jari, yana mai cewa bangaren na dauke da fiye da kashi 90 cikin 100 na dukkanin kasuwancin Nijeriya na kasa da kasa ta fuskar girma.

Tashoshin
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Umurci Kamfanonin Rarraba Wutar Lantarki Su Biya Biliyan ₦55.42

Majalisar Wakilai Ta Umurci Kamfanonin Rarraba Wutar Lantarki Su Biya Biliyan ₦55.42

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.