Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Zartarwa na Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA), Dakta Abubakar Dantsoho, ya ce da sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa, tsarin tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya zai shiga sabon mataki tare da zama jagora a harkar sufurin ruwa a nahiyar Afirka.
Dantsoho ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron Zuba Jari na Tattalin Arzikin Teku (Blue Economy Inbestment Summit) da aka gudanar a Abuja, inda ya ce tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya za su taka muhimmiyar rawa wajen jawo manyan masu zuba jari da kuma hanzarta bunkasar tattalin arziki.
Sai dai ya danganta sauyin da ake samu a bangaren harkar ruwa da tasirin Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Teku, Dakta Adegboyega Oyetola, da kuma sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa.
Ya kuma tabbatar wa masu zuba jari cewa Nijeriya na da karfin zama jagora a tattalin arzikin tekun Afirka (blue economy), yana mai cewa gyare-gyaren gwamnati da kuma karuwar shigar masu zaman kansu su ne manyan ginshikan wannan sauyi.
Ya ce dole ne Nijeriya ta mayar da hankali wajen amfani da albarkatun tekunta yadda ya kamata domin cimma manufofin ci gaban duniya mai dorewa.
“Lokaci ya yi da za a sauya tsarin tattalin arzikin Nijeriya zuwa yadda za a yi cikakken amfani da albarkatun tekunmu. Idan aka yi amfani da tsarin tashoshin jiragen ruwa yadda ya kamata, zai iya zama babban ginshiki na bunkasar tattalin arziki,” in ji shi.
Shugaban NPA ya bayyana cewa matsayi na Nijeriya a taswirar duniya, yawan al’umma da karfin tattalin arziki suna ba ta damar zama cibiyar harkar ruwa a Yammacin Afirka, kamar kasashe irin su Singapore da Morocco.
“Saboda matsayinta na dabaru, girman kasuwa da karfin tattalin arziki, Nijeriya na da damar zama cibiyar harkar jiragen ruwa ta Yammacin Afirka,” in ji shi.
Duk da wadannan damar, Dantsoho ya nuna damuwa cewa a halin yanzu Nijeriya na sarrafa kusan kashi 25 cikin 100 ne kawai na zirga-zirgar kaya a yankin, duk da cewa tana dauke da fiye da kashi 60 cikin 100 na GDP na Yammacin Afirka.
“Abin damuwa ne cewa Nijeriya, duk da cewa tana da sama da kashi 60 cikin 100 na GDP na Yammacin Afirka, tana sarrafa kusan kashi 25 cikin 100 ne kawai na jigilar kaya a yankin. Wannan a fili yana nuna cewa ba mu yi amfani da cikakken damar da muke da ita ba,” in ji shi.
Dantsoho ya jaddada cewa gasa a harkar sufurin ruwa ta duniya na bukatar ingantaccen aiki, farashi mai gasa da kuma kyakkyawar hadin kai tsakanin yankunan cikin kasa da tashoshin ruwa, yana mai cewa dole ne tashoshin Nijeriya su ci gaba da sabawa da sauye-sauyen da ke faruwa a harkar sufurin ruwa a duniya.
“Idan aka ci gaba da aiwatar da wadannan tsare-tsare yadda ya kamata, tsarin tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya zai shiga sabon mataki tare da zama jagora a harkar sufurin ruwa a Afirka,” in ji shi.
Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Teku, Adegboyega Oyetola, a jawabinsa na farko, ya ce albarkatun da Nijeriya ke da su, ciki har da bakin tekun ta mai tsawon kilomita 823 da manyan hanyoyin ruwa na cikin kasa, suna ba ta damar jagorantar wannan bangare.
“Da bakin teku mai tsawon kilomita 823, manyan hanyoyin ruwa na cikin kasa da kuma matsayi mai muhimmanci a Tekun Guinea, Nijeriya na da damar musamman wajen amfani da albarkatun tattalin arzikin ruwa,” in ji Oyetola.
Ya kara da cewa sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke yi sun inganta hadin kai, karfafa tsaron teku da kuma kara amincewar masu zuba jari, yana mai cewa bangaren na dauke da fiye da kashi 90 cikin 100 na dukkanin kasuwancin Nijeriya na kasa da kasa ta fuskar girma.















Discussion about this post