ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashoshin Ruwan Nijeriya Za Su Yi Daidai Da Na Manyan Kasashen Duniya – Dantsoho

by Bello Hamza
1 month ago
Tashoshin

Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Zartarwa na Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA), Dakta Abubakar Dantsoho, ya ce da sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa, tsarin tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya zai shiga sabon mataki tare da zama jagora a harkar sufurin ruwa a nahiyar Afirka.

Dantsoho ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron Zuba Jari na Tattalin Arzikin Teku (Blue Economy Inbestment Summit) da aka gudanar a Abuja, inda ya ce tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya za su taka muhimmiyar rawa wajen jawo manyan masu zuba jari da kuma hanzarta bunkasar tattalin arziki.

Sai dai ya danganta sauyin da ake samu a bangaren harkar ruwa da tasirin Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Teku, Dakta Adegboyega Oyetola, da kuma sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa.

ADVERTISEMENT

Ya kuma tabbatar wa masu zuba jari cewa Nijeriya na da karfin zama jagora a tattalin arzikin tekun Afirka (blue economy), yana mai cewa gyare-gyaren gwamnati da kuma karuwar shigar masu zaman kansu su ne manyan ginshikan wannan sauyi.

Ya ce dole ne Nijeriya ta mayar da hankali wajen amfani da albarkatun tekunta yadda ya kamata domin cimma manufofin ci gaban duniya mai dorewa.

LABARAI MASU NASABA

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

“Lokaci ya yi da za a sauya tsarin tattalin arzikin Nijeriya zuwa yadda za a yi cikakken amfani da albarkatun tekunmu. Idan aka yi amfani da tsarin tashoshin jiragen ruwa yadda ya kamata, zai iya zama babban ginshiki na bunkasar tattalin arziki,” in ji shi.

Shugaban NPA ya bayyana cewa matsayi na Nijeriya a taswirar duniya, yawan al’umma da karfin tattalin arziki suna ba ta damar zama cibiyar harkar ruwa a Yammacin Afirka, kamar kasashe irin su Singapore da Morocco.

“Saboda matsayinta na dabaru, girman kasuwa da karfin tattalin arziki, Nijeriya na da damar zama cibiyar harkar jiragen ruwa ta Yammacin Afirka,” in ji shi.

Duk da wadannan damar, Dantsoho ya nuna damuwa cewa a halin yanzu Nijeriya na sarrafa kusan kashi 25 cikin 100 ne kawai na zirga-zirgar kaya a yankin, duk da cewa tana dauke da fiye da kashi 60 cikin 100 na GDP na Yammacin Afirka.

“Abin damuwa ne cewa Nijeriya, duk da cewa tana da sama da kashi 60 cikin 100 na GDP na Yammacin Afirka, tana sarrafa kusan kashi 25 cikin 100 ne kawai na jigilar kaya a yankin. Wannan a fili yana nuna cewa ba mu yi amfani da cikakken damar da muke da ita ba,” in ji shi.

Dantsoho ya jaddada cewa gasa a harkar sufurin ruwa ta duniya na bukatar ingantaccen aiki, farashi mai gasa da kuma kyakkyawar hadin kai tsakanin yankunan cikin kasa da tashoshin ruwa, yana mai cewa dole ne tashoshin Nijeriya su ci gaba da sabawa da sauye-sauyen da ke faruwa a harkar sufurin ruwa a duniya.

“Idan aka ci gaba da aiwatar da wadannan tsare-tsare yadda ya kamata, tsarin tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya zai shiga sabon mataki tare da zama jagora a harkar sufurin ruwa a Afirka,” in ji shi.

Ministan Harkokin Ruwa da Tattalin Arzikin Teku, Adegboyega Oyetola, a jawabinsa na farko, ya ce albarkatun da Nijeriya ke da su, ciki har da bakin tekun ta mai tsawon kilomita 823 da manyan hanyoyin ruwa na cikin kasa, suna ba ta damar jagorantar wannan bangare.

“Da bakin teku mai tsawon kilomita 823, manyan hanyoyin ruwa na cikin kasa da kuma matsayi mai muhimmanci a Tekun Guinea, Nijeriya na da damar musamman wajen amfani da albarkatun tattalin arzikin ruwa,” in ji Oyetola.

Ya kara da cewa sauye-sauyen da gwamnatin tarayya ke yi sun inganta hadin kai, karfafa tsaron teku da kuma kara amincewar masu zuba jari, yana mai cewa bangaren na dauke da fiye da kashi 90 cikin 100 na dukkanin kasuwancin Nijeriya na kasa da kasa ta fuskar girma.

Tashoshin
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe
Tattalin Arziki

Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

June 6, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su
Tattalin Arziki

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Umurci Kamfanonin Rarraba Wutar Lantarki Su Biya Biliyan ₦55.42

Majalisar Wakilai Ta Umurci Kamfanonin Rarraba Wutar Lantarki Su Biya Biliyan ₦55.42

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.