Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya sake jaddada goyon bayan jama’a ga jami’an tsaro da ke fafatawa da ƴan ta’adda, tare da gargaɗin al’umma da su guji bayar da bayanan sirri kan motsin sojoji.
Gwamnan ya yi wannan kira ne yayin da ya ziyarci Sojoji uku da suka jikkata sakamakon harin kwanton ɓauna da ƴan bindiga suka kai wa dakarun, inda ya bayyana cewa maharan sun samu damar kai harin ne bisa bayanan sirri daga wasu cikin jama’a da ke taimaka musu.
- Kwararru Sun Ankarar Da Manoma Kan Tunkarar Noman Kakar Bana
- Wang Yi Da Takwaransa Na Kamaru Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyyar Kasashen 2
Ya bayyana irin wannan aiki a matsayin cin amanar ƙasa, yana mai cewa jami’an tsaro na yin ƙoƙari sosai wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
A yayin ziyarar, kwamandan Rundunar Sojojin 22 Armoured Brigade da ke Sobi Barracks a Ilorin, da Birgediya Janar Nicholas Nemetne Rume, tare da babban daraktan asibitin, Farfesa Abdullah Yusuf, ne suka tarɓi gwamnan.
Gwamna AbdulRazaq ya jajanta wa iyalan sojojin uku da suka rasa rayukansu a harin, inda ya sanar da bayar da tallafin ₦20m ga kowanne iyali (jimillar ₦60m), sannan ya ware ₦5m ga kowanne daga cikin sojojin uku da ke jinya. Ya ƙara da cewa hakan na nuna irin sadaukarwar da jami’an tsaro ke yi wajen kare kasa, yana kuma kira ga ’yan Nijeriya da su ci gaba da mara musu baya a yaƙi da ta’addanci.















Discussion about this post