ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararru Sun Ankarar Da Manoma Kan Tunkarar Noman Kakar Bana

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 months ago
Manoma

Wasu kwararru a fannin aikin noma a kasar nan, sun bukaci manoman kasar, da su fara shirye-shiryen tunkarar aikin noma a kakar noma ta 2026.

Sun bayar da wannan shawara ce, musamman domin a kara habaka samar da wadataccen abinci a kasar tare da kuma samar da girbin amfanin gona mai yawan gaske.

  • Tallafin Abinci Na Gaggawa Daga Sin Ya Isa Togo
  • 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya

Kazalika, sun kuma yi kira a gare su da su rungumi dabarun yin noma na zamani, domin kara habaka sana’ar tasu.

ADVERTISEMENT

Kwararrun, sun yi wannan kira ne a taron da aka gudanar a cikin kasidun da suka gabatar daban-daban, domin yin nazarin shirin aikin noma na bana,

Kungiyar AGAN ce, ta shirya taron a ma’aikatar aikin noma ta Jihar Neja.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Jami’in kungiyar a jihar, wanda kuma shi ne babban shugaban kungiyar Hussaini Iliyasu, ya bayyana hakan ne a jawabinsa a wajen taron.

Mahalarta taron, sun tattauna kan dabarun da ya kamata a dauka, domin a kara habaka fannnin na aikin noma, wanda hakan zai kuma sanya, manoman kasar su samu girbi mai yawa.

Ya bayyana cewa, daya daga cikin kalubalen da moman kasar ke ci gaba da fuskanta shi ne, rashin iya zuba takin zamani a shukarsu.

Ya kara da cewa, kungiyar na kuma ci gaba da yin kokarin taimaka wa manoman, domin kauce wa wannan kalubale na rashin iya zuba takin.

A cewarsa, manoman na kawai sayo takin ne, su kuma zuba a shukarsu, ko kuma idan gwamnati ta tallafa musu da takin, sai kawai su zuba shi, ba tare da bin ka’ida ba.

“Mun kirkiro da tsarin yin gwajin kasar gona, domin a taimaka wa manoman yadda za su noma gonakinsu”.

“Muna kuma koya wa manoman yadda za su rage yin dogaro kan yin amfani da takin zamanin da ke dauke da sanadarai, inda ya kara da cewa, a yanzu, muna kai wa manoman takin gargajiya, wanda ke dauke da sanadaran da ke taimaka wa amfanin da aka shuka”.

Ya sanar da cewa, yin amfani da takin na gargajiya, ya kara habaka amfanin gona da manoman suka shuka, wanda kuma ke kara lafiyar amfanin da aka shuka.

Shi kuwa, Dakta Gana Andrew Kolo, Darakta a cibiyar gudanar da bincike kan hatsi ta kasa da ke yankin Badeggi a Jihar Neja ya sanar da cewa, saboda sauyin yanayi da ake fuskanta a duniya, cibiyar ta kirkiro da wata sabuwar kimiyya wadda nan ba da jimawa ba, za ta gabatarwa da manoman kasar, wadda za ta taimaka wa manoman girbe amfanin gona mai yawa.

Ya kara da cewa, cibiyar ta kuma samar da dabaru, kan yadda manoman kasar, za su rinka zuba takin gargajiya a shukarsu wanda hakan zai kara inganta kasar nomansu.

Kolo ya kuma shawarci manoman cewa, bisa hasashen da hukumar kula da yanayi ta kasa ta yi na samun saukar ruwan damina da wuri, ya kamata manoman kasar, su fara shirye-shiryen fara yin noma.

Ya kuma bukace su, da su tabbatar da sun samu ingantaccen Irin noma, musamman Irin Shinkafa da Waken Soya.

Ya kuma bukace su da su tabbatar da sun shuka Irin noma na gajeren zango wanda ko da a ce ruwan saman bai yi nisa ba, za su iya kauce wa fuskantar matsala.

Manoma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta Nuna Yanzu Duniya Ta Fi Mutunta Sin Fiye Da Amurka

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta Nuna Yanzu Duniya Ta Fi Mutunta Sin Fiye Da Amurka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.