ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararru Sun Ankarar Da Manoma Kan Tunkarar Noman Kakar Bana

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 months ago
Manoma

Wasu kwararru a fannin aikin noma a kasar nan, sun bukaci manoman kasar, da su fara shirye-shiryen tunkarar aikin noma a kakar noma ta 2026.

Sun bayar da wannan shawara ce, musamman domin a kara habaka samar da wadataccen abinci a kasar tare da kuma samar da girbin amfanin gona mai yawan gaske.

  • Tallafin Abinci Na Gaggawa Daga Sin Ya Isa Togo
  • 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya

Kazalika, sun kuma yi kira a gare su da su rungumi dabarun yin noma na zamani, domin kara habaka sana’ar tasu.

ADVERTISEMENT

Kwararrun, sun yi wannan kira ne a taron da aka gudanar a cikin kasidun da suka gabatar daban-daban, domin yin nazarin shirin aikin noma na bana,

Kungiyar AGAN ce, ta shirya taron a ma’aikatar aikin noma ta Jihar Neja.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Jami’in kungiyar a jihar, wanda kuma shi ne babban shugaban kungiyar Hussaini Iliyasu, ya bayyana hakan ne a jawabinsa a wajen taron.

Mahalarta taron, sun tattauna kan dabarun da ya kamata a dauka, domin a kara habaka fannnin na aikin noma, wanda hakan zai kuma sanya, manoman kasar su samu girbi mai yawa.

Ya bayyana cewa, daya daga cikin kalubalen da moman kasar ke ci gaba da fuskanta shi ne, rashin iya zuba takin zamani a shukarsu.

Ya kara da cewa, kungiyar na kuma ci gaba da yin kokarin taimaka wa manoman, domin kauce wa wannan kalubale na rashin iya zuba takin.

A cewarsa, manoman na kawai sayo takin ne, su kuma zuba a shukarsu, ko kuma idan gwamnati ta tallafa musu da takin, sai kawai su zuba shi, ba tare da bin ka’ida ba.

“Mun kirkiro da tsarin yin gwajin kasar gona, domin a taimaka wa manoman yadda za su noma gonakinsu”.

“Muna kuma koya wa manoman yadda za su rage yin dogaro kan yin amfani da takin zamanin da ke dauke da sanadarai, inda ya kara da cewa, a yanzu, muna kai wa manoman takin gargajiya, wanda ke dauke da sanadaran da ke taimaka wa amfanin da aka shuka”.

Ya sanar da cewa, yin amfani da takin na gargajiya, ya kara habaka amfanin gona da manoman suka shuka, wanda kuma ke kara lafiyar amfanin da aka shuka.

Shi kuwa, Dakta Gana Andrew Kolo, Darakta a cibiyar gudanar da bincike kan hatsi ta kasa da ke yankin Badeggi a Jihar Neja ya sanar da cewa, saboda sauyin yanayi da ake fuskanta a duniya, cibiyar ta kirkiro da wata sabuwar kimiyya wadda nan ba da jimawa ba, za ta gabatarwa da manoman kasar, wadda za ta taimaka wa manoman girbe amfanin gona mai yawa.

Ya kara da cewa, cibiyar ta kuma samar da dabaru, kan yadda manoman kasar, za su rinka zuba takin gargajiya a shukarsu wanda hakan zai kara inganta kasar nomansu.

Kolo ya kuma shawarci manoman cewa, bisa hasashen da hukumar kula da yanayi ta kasa ta yi na samun saukar ruwan damina da wuri, ya kamata manoman kasar, su fara shirye-shiryen fara yin noma.

Ya kuma bukace su, da su tabbatar da sun samu ingantaccen Irin noma, musamman Irin Shinkafa da Waken Soya.

Ya kuma bukace su da su tabbatar da sun shuka Irin noma na gajeren zango wanda ko da a ce ruwan saman bai yi nisa ba, za su iya kauce wa fuskantar matsala.

Manoma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta Nuna Yanzu Duniya Ta Fi Mutunta Sin Fiye Da Amurka

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta Nuna Yanzu Duniya Ta Fi Mutunta Sin Fiye Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.