ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararru Sun Ankarar Da Manoma Kan Tunkarar Noman Kakar Bana

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
Manoma

Wasu kwararru a fannin aikin noma a kasar nan, sun bukaci manoman kasar, da su fara shirye-shiryen tunkarar aikin noma a kakar noma ta 2026.

Sun bayar da wannan shawara ce, musamman domin a kara habaka samar da wadataccen abinci a kasar tare da kuma samar da girbin amfanin gona mai yawan gaske.

  • Tallafin Abinci Na Gaggawa Daga Sin Ya Isa Togo
  • 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya

Kazalika, sun kuma yi kira a gare su da su rungumi dabarun yin noma na zamani, domin kara habaka sana’ar tasu.

ADVERTISEMENT

Kwararrun, sun yi wannan kira ne a taron da aka gudanar a cikin kasidun da suka gabatar daban-daban, domin yin nazarin shirin aikin noma na bana,

Kungiyar AGAN ce, ta shirya taron a ma’aikatar aikin noma ta Jihar Neja.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Jami’in kungiyar a jihar, wanda kuma shi ne babban shugaban kungiyar Hussaini Iliyasu, ya bayyana hakan ne a jawabinsa a wajen taron.

Mahalarta taron, sun tattauna kan dabarun da ya kamata a dauka, domin a kara habaka fannnin na aikin noma, wanda hakan zai kuma sanya, manoman kasar su samu girbi mai yawa.

Ya bayyana cewa, daya daga cikin kalubalen da moman kasar ke ci gaba da fuskanta shi ne, rashin iya zuba takin zamani a shukarsu.

Ya kara da cewa, kungiyar na kuma ci gaba da yin kokarin taimaka wa manoman, domin kauce wa wannan kalubale na rashin iya zuba takin.

A cewarsa, manoman na kawai sayo takin ne, su kuma zuba a shukarsu, ko kuma idan gwamnati ta tallafa musu da takin, sai kawai su zuba shi, ba tare da bin ka’ida ba.

“Mun kirkiro da tsarin yin gwajin kasar gona, domin a taimaka wa manoman yadda za su noma gonakinsu”.

“Muna kuma koya wa manoman yadda za su rage yin dogaro kan yin amfani da takin zamanin da ke dauke da sanadarai, inda ya kara da cewa, a yanzu, muna kai wa manoman takin gargajiya, wanda ke dauke da sanadaran da ke taimaka wa amfanin da aka shuka”.

Ya sanar da cewa, yin amfani da takin na gargajiya, ya kara habaka amfanin gona da manoman suka shuka, wanda kuma ke kara lafiyar amfanin da aka shuka.

Shi kuwa, Dakta Gana Andrew Kolo, Darakta a cibiyar gudanar da bincike kan hatsi ta kasa da ke yankin Badeggi a Jihar Neja ya sanar da cewa, saboda sauyin yanayi da ake fuskanta a duniya, cibiyar ta kirkiro da wata sabuwar kimiyya wadda nan ba da jimawa ba, za ta gabatarwa da manoman kasar, wadda za ta taimaka wa manoman girbe amfanin gona mai yawa.

Ya kara da cewa, cibiyar ta kuma samar da dabaru, kan yadda manoman kasar, za su rinka zuba takin gargajiya a shukarsu wanda hakan zai kara inganta kasar nomansu.

Kolo ya kuma shawarci manoman cewa, bisa hasashen da hukumar kula da yanayi ta kasa ta yi na samun saukar ruwan damina da wuri, ya kamata manoman kasar, su fara shirye-shiryen fara yin noma.

Ya kuma bukace su, da su tabbatar da sun samu ingantaccen Irin noma, musamman Irin Shinkafa da Waken Soya.

Ya kuma bukace su da su tabbatar da sun shuka Irin noma na gajeren zango wanda ko da a ce ruwan saman bai yi nisa ba, za su iya kauce wa fuskantar matsala.

Manoma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta Nuna Yanzu Duniya Ta Fi Mutunta Sin Fiye Da Amurka

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta Nuna Yanzu Duniya Ta Fi Mutunta Sin Fiye Da Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.