ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwararru Sun Ankarar Da Manoma Kan Tunkarar Noman Kakar Bana

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 months ago
Manoma

Wasu kwararru a fannin aikin noma a kasar nan, sun bukaci manoman kasar, da su fara shirye-shiryen tunkarar aikin noma a kakar noma ta 2026.

Sun bayar da wannan shawara ce, musamman domin a kara habaka samar da wadataccen abinci a kasar tare da kuma samar da girbin amfanin gona mai yawan gaske.

  • Tallafin Abinci Na Gaggawa Daga Sin Ya Isa Togo
  • 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya

Kazalika, sun kuma yi kira a gare su da su rungumi dabarun yin noma na zamani, domin kara habaka sana’ar tasu.

ADVERTISEMENT

Kwararrun, sun yi wannan kira ne a taron da aka gudanar a cikin kasidun da suka gabatar daban-daban, domin yin nazarin shirin aikin noma na bana,

Kungiyar AGAN ce, ta shirya taron a ma’aikatar aikin noma ta Jihar Neja.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Jami’in kungiyar a jihar, wanda kuma shi ne babban shugaban kungiyar Hussaini Iliyasu, ya bayyana hakan ne a jawabinsa a wajen taron.

Mahalarta taron, sun tattauna kan dabarun da ya kamata a dauka, domin a kara habaka fannnin na aikin noma, wanda hakan zai kuma sanya, manoman kasar su samu girbi mai yawa.

Ya bayyana cewa, daya daga cikin kalubalen da moman kasar ke ci gaba da fuskanta shi ne, rashin iya zuba takin zamani a shukarsu.

Ya kara da cewa, kungiyar na kuma ci gaba da yin kokarin taimaka wa manoman, domin kauce wa wannan kalubale na rashin iya zuba takin.

A cewarsa, manoman na kawai sayo takin ne, su kuma zuba a shukarsu, ko kuma idan gwamnati ta tallafa musu da takin, sai kawai su zuba shi, ba tare da bin ka’ida ba.

“Mun kirkiro da tsarin yin gwajin kasar gona, domin a taimaka wa manoman yadda za su noma gonakinsu”.

“Muna kuma koya wa manoman yadda za su rage yin dogaro kan yin amfani da takin zamanin da ke dauke da sanadarai, inda ya kara da cewa, a yanzu, muna kai wa manoman takin gargajiya, wanda ke dauke da sanadaran da ke taimaka wa amfanin da aka shuka”.

Ya sanar da cewa, yin amfani da takin na gargajiya, ya kara habaka amfanin gona da manoman suka shuka, wanda kuma ke kara lafiyar amfanin da aka shuka.

Shi kuwa, Dakta Gana Andrew Kolo, Darakta a cibiyar gudanar da bincike kan hatsi ta kasa da ke yankin Badeggi a Jihar Neja ya sanar da cewa, saboda sauyin yanayi da ake fuskanta a duniya, cibiyar ta kirkiro da wata sabuwar kimiyya wadda nan ba da jimawa ba, za ta gabatarwa da manoman kasar, wadda za ta taimaka wa manoman girbe amfanin gona mai yawa.

Ya kara da cewa, cibiyar ta kuma samar da dabaru, kan yadda manoman kasar, za su rinka zuba takin gargajiya a shukarsu wanda hakan zai kara inganta kasar nomansu.

Kolo ya kuma shawarci manoman cewa, bisa hasashen da hukumar kula da yanayi ta kasa ta yi na samun saukar ruwan damina da wuri, ya kamata manoman kasar, su fara shirye-shiryen fara yin noma.

Ya kuma bukace su, da su tabbatar da sun samu ingantaccen Irin noma, musamman Irin Shinkafa da Waken Soya.

Ya kuma bukace su da su tabbatar da sun shuka Irin noma na gajeren zango wanda ko da a ce ruwan saman bai yi nisa ba, za su iya kauce wa fuskantar matsala.

Manoma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Manoma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta Nuna Yanzu Duniya Ta Fi Mutunta Sin Fiye Da Amurka

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta Nuna Yanzu Duniya Ta Fi Mutunta Sin Fiye Da Amurka

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.