Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya gargadi shugabannin APC a jihar da su guji duk wani aikin da ya saBa wa dokokin jam’iyya.
Hakan na zuwa ne yayin da ya sanar da cewa kwamishinonin jihar za su kasance shugabannin Kwamitin Shirya Taron ZaBen Jam’iyya a kananan hukumomi.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a taron masu ruwa da tsaki na APC da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Minna, inda ya ce daukar wannan mataki ya zama dole sakamakon karewar wa’adin shugabannin jam’iyyar APC na jihar.
Ya ce kwamishinonin za su dauki alhakin tattara cikakken jerin sunayen ‘yan jam’iyya daga kananan hukumominsu, tare da tabbatar da yin aiki kafada da kafada da muhimman masu ruwa da tsaki.
Bago ya jaddada cewa dole ne kwamitocin daidaita taron zaBen su bi yarjejeniyar da aka cimma tsakanin manyan masu ruwa da tsaki a kowace karamar hukuma domin tabbatar da gudanar da zaBe cikin lumana ba tare da rikici ba.
Ya kuma shawarci kwamishinonin da kada su yi sakaci ko sassauci, yana mai cewa duk wanda aka samu da laifi za a hukunta shi yadda ya kamata. Ya kara da cewa APC jam’iyya ce mai biyayya ga doka, kuma “ba za ta lamunci ayyukan da suka saBa wa jam’iyya ko manyan laifuka daga kowane dan jam’iyya ba.”
A nasa Bangaren, mataimakin shugaban APC na shiyyar Arewa ta Tsakiya, Mu’azu Bawa Rijau, ya ce jam’iyyar bayan taron Kwamitin Zartarwa na Kasa (NEC), ta yanke shawarar cewa dukkan zaBukan jam’iyya za a gudanar da su ta hanyar maslaha (consensus) a matakan mazaBu, karamar hukuma, jiha, shiyya da kasa, kuma ya kamata dukkan mambobi su amince da hakan.
Bawa ya kuma sake jaddada goyon bayan jam’iyyar ga gwamnan, yana mai cewa yana gudanar da aiki abin yabawa a fannoni daban-daban.















Discussion about this post