Gwamnan Jihar Katsina, Malam DIkko Umar Radda, ya rantsar da Khadi Mustapha Salis a matsayin sabon alkali wato Khadi, na kotun daukaka kara ta Shari’ar Musulunci ta Jihar Katsina.
An gudanar da bikin rantsarwar ne a dakin taro na gidan gwamnati, inda manyan jami’ai daga Bangaren shari’a da Bangaren zartaswa da na majalisa suka halarta, tare da sarakuna da malamai da kuma ‘yan’uwan sabon alkalin.
- Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 3
- Babu Wani Abu A Alkur’ani Da Ya Zama Maimaici, Komai Yana Da Ma’anarsa
A jawabinsa, Gwamna Radda ya bukaci sabon Khadin da ya tabbatar da gaskiya, adalci da tsaron Allah wajen gudanar da aikinsa.
Gwamnan ya bayyana nadin nasa a matsayin wani muhimmin mataki na karfafa tsarin shari’ar Musulunci da kuma inganta samar da adalci a fadin jihar.
Ya taya sabon Khadin murna tare da yaba wa Hukumar Kula da Ayyukan Shari’a ta Jihar Katsina bisa gudanar da sahihin tsari na zaBe bisa cancanta da kwarewa.
Yayin da yake tunatar da sabon alkalin nauyin da ke gabansa, gwamnan ya bukace shi da ya rika tuna rantsuwar da ya yi a dukkanin ayyukansa.
Gwamna Radda ya jaddada cewa dole ne a rika yin adalci ba tare da tsoro ko son zuciya ba, tare da tunatar da sabon Khadin cewa mukaminsa amana ce mai tsarki a gaban Allah da al’umma.
Ya kuma ce shugaban shari’a shi ne gatan talakawa na karshe, inda ya kara da cewa amincewar jama’a na dogara ne ka gaskiya da jajircewar jami’an shari’a.
Gwamnan ya kuma sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da tallafa wa Bangaren shari’a tare da karfafa kyakkyawar hudda tsakanin Bangarori uku na gwamnati domin tabbatar da zaman lafiya da doka da oda da kuma adalci a Jihar Katsina.















Discussion about this post