Hukumar Kwastam ta Nijeriya, reshen Jihar Kebbi ta bude kan iyakokin Kamba da Tsamiya a Kananan Hukumomin Dandi da Bagudo na jihar zuwa Jamhuriyar Benin da Jamhuriyar Nijar, domin saukaka kasuwanci tsakanin kasashen biyu.
An rufe iyakokin ne, a kan kasashen biyu sakamakon karuwar rashin tsaro a yankunan kan iyaka.
Sai dai, a yanzu an bude iyakokin bayan tattaunawa da yarjejeniyoyin da aka cimma tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Benin.
Da yake bude iyakokin kasashen biyu a ranar Litinin, Kwanturolan Hukumar Kwastam na Jihar Kebbi, Mahmud Matawalle Ibrahim, ya ce; an bude iyakokin ne, bisa amincewar shugaban kasa, domin bayar da damar jigilar kayayyaki daga kan iyakar Tsamiya zuwa Jamhuriyar Nijar ta kan iyakar Kamba da ke Jihar Kebbi.
Ya ce, da wannan ne aka fitar da da yawa daga cikin manyan motocin da suka makale daga Jamhuriyar Benin a Tsamiya, domin shiga kan iyakar Jamhuriyar Nijar ta Tunga Jado ta kan iyakar Kamba a Jihar Kebbi.
Kazalika, ya bayyana cewa; sake bude iyakokin zai saukaka tare da bunkasa harkokin kasuwanci a tsakanin kasashen da kuma bunkasa harkokin tsaro a yayin da suke da niyyar kiyaye yarjejeniyoyin da kuma tabbatar da gudanar da harkokin kasuwanci cikin sauki.















Discussion about this post