Gwamnatin Nijeriya ta gode wa Masarautar Saudiyya bisa sakin ƴan Nijeriya uku da aka tsare a Jeddah tun watan Agustan 2025, bayan samunsu da laifin da daga baya aka gano cewa an ƙaƙabawa musu ne ba tare da saninsu ba. A wata sanarwa da mai bai wa Ministan Harkokin Waje shawara kan kafafen watsa labarai, Alkasim Abdulkadir, ya fitar a ranar Laraba, yana mai bayyana cewa an wanke su daga duk wata tuhuma bayan cikakken bincike.
Sanarwar ta ce waɗanda aka kama su ne Abdulhamid Sadieq, da Maryam Abdullahi da Bahijah Abdullahi, waɗanda ake zargin an haɗa musu haramtattun kayayyaki ne ta hanyar masu makircin harƙyallar miyagun ƙwayoyi a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano ba tare da sanin fasinjojin ba. Ofishin Jakadancin Nijeriya a Jeddah, ƙarƙashin Jakada Muazam Nayaya, ya shiga lamarin tun daga farko tare da tuntubar hukumomin Saudiyya domin kare mutanen.
- Ko Kwalliya Za Ta Biya Kuɗin Sabulu Kan Sauye-sauyen Tinubu Na Inganta Tsaro A Nijeriya?
- Shugaban Faransa Emmanuel Macron Ya Sauka Beijing Domin Ziyarar Aiki
Bayan tsare su, hukumar NDLEA daga Nijeriya ta shiga bincike tare da tabbatar da cewa ba su da hannu cikin lamarin. Sanarwar ta bayyana cewa ofishin jakadancin ya ci gaba da kai ziyara gidan yari, ya bayar da taimakon lauya, sannan yana tuntubar hukumomin Saudiyya har zuwa lokacin da aka wanke su. An saki Maryam da Bahijah a ranar 14 da 15 ga Satumba 2025, inda suka dawo gida ranar 5 ga Nuwamba.
Abdulkadir ya ce an kuma ɗage hani na tafiya da aka ƙaƙabawa wa Abdulhamid Sadieq a ranar 2 ga Disamba 2025, kuma ana kammala shirye-shiryen dawowarsa gida. Ya ce sakin mutanen ya nuna jajircewar Nijeriya wajen kare ƴan ƙasar a ƙasashen waje, bisa tsarin 4D na shugaban ƙasa Bola Tinubu.














