• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Bai Wa Dalibai Hutun Zabe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Bauchi Ta Bai Wa Dalibai Hutun Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Bauchi ta sanar da ba da hutun kwanaki biyu ga daliban makarantun jeka-ka-dawo da suke karkashinta domin samun sararin gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya a ranar Asabar.

Kwamishiniyar ma’aikatar ilimi ta jihar, Dakta Jamila Muhammad Dahiru ce, ta bayyana hakan ga manema labarai a Bauchi.

  • Me Ya Sa Samari Ke Wa ‘Yan Matan Yanzu Kallon Zawarawa?
  • Buhari Da Tsofaffin Shugabannin Kasa Sun Bukaci ‘Yan Takara Su Karbi Sakamakon Zabe

Ta ce, an ba da hutun ne domin Malamai da iyayen yaran su samu damar yin zabe.

Sannan kuma wasu daliban za su yi tafiya da iyayensu zuwa garuruwa da kauyukansu domin kada kuri’a.

Sannan ta ce a cikin daliban akwai wadanda shekarunsu ya kai na jefa kuri’a don haka wannan hutun zai ba su damar yin zabe.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

Kazalika, ta sanar da cewa gwamnatin ta kuma sake ba da hutun kwanaki biyu ga daliban makarantun jeka-ka-dawo a lokacin zaben gwamnan Jihar da na ‘yan majalisun dokoki da zai gudana a ranar 11 ga watan Maris.

“Bisa wannan, daliban makarantun jeka-ka-dawo za su kasance a gida a ranar Juma’a 24 da Litinin 27 ga watan Fabrairu, 2023 a matsayin hutun zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da za a gudanar a ranar Asabar.

“Ga zaben gwamna da na ‘yan majalisun jiha kuma, dalibai za su kasance a gida a ranar Juma’a 10 da ranar Litinin 13 ga watan Maris 2023, don haka harkokin karatu za su kankama a ranar Talata 14 ga watan Maris.”

Jamila ta ce, daliban makarantun kwana da suke jihar za su kasance a cikin makarantunsu a wannan lokaci.

Kwamishiniyar ta yi amfani da wannan damar wajen nanata aniyar gwamnatin Jihar Bauchi na inganta ilimi, walwala da jin dadin Malamai gami da bayar da ilimi mai nagarta.

Ta yi fatan a yi zabe cikin kwanciyar hankali a dukkanin matakai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dakta JamilaDalibaiHutuIlimiKwamishiniyaMakarantaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyoyi Magoya Bayan Buhari-Osinbajo Sun Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Zabi Atiku Na Jam’iyyar PDP

Next Post

INEC Ta Fara Raba Kayan Aikin Zabe A Adamawa

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

2 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

3 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

5 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

5 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

6 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

9 hours ago
Next Post
INEC Ta Fara Raba Kayan Aikin Zabe A Adamawa

INEC Ta Fara Raba Kayan Aikin Zabe A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.