Gwamnatin Jihar Kebbi ta amince da kashe sama da Naira biliyan 2.07 a watan Agusta 2026 domin biyan wasu alawus-alawus, basussuka da sauran hakkokin ma’aikatan manyan makarantun jihar. Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi, Isah Abubakar Tunga, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Birnin Kebbi.
Kwamishinan ya ce Gwamna Nasir Idris ya amince da sakin N172.15m domin biyan alawus-alawus na CATA da CONTTA ga kungiyoyin ASUU, SSANU, NASU da NAAT na Jami’ar Abdullahi Fodiyo ta Kimiyya da Fasaha, Aliero (AFUSTA).
Ya kuma ce gwamnati ta amince da shigar da CATA da CONTTA cikin tsarin biyan kudin wata-wata na AFUSTA, wanda zai kai kusan N2.066bn a duk shekara. Haka kuma, an amince da biyan N151.52m na bashin karin matakin shekara-shekara ga ma’aikatan jami’ar.
A wani bangare, gwamnatin jihar ta raba sabbin motocin bas na Coaster masu kujeru 32 da na’urar sanyaya iska ga manyan makarantu bakwai, domin saukaka zirga-zirgar dalibai. An kashe kusan N1.75bn wajen sayen motocin bas din.Makarantun da suka amfana da motocin sun hada da AFUSTA, Kwalejin Ilimi ta Adamu Augie da ke Argungu, kwalejojin lafiya na Birnin Kebbi da Ambursa, Kwalejin Kimiyyar Lafiya da Fasaha ta Jega, Polytechnic ta Jihar Kebbi da ke Dakingari, da Kwalejin Kwarewa kan Shari’a da Nazarin Shari’a ta Yauri.
Haka kuma, Gwamna Nasir Idris ya amince da nadin Dr. Zayyanu Umar a matsayin shugaba na Kwalejin Ilimi ta Adamu Augie, Argungu.
Kwamishinan ya yabawa gwamnatin jihar bisa kokarin inganta harkar ilimi mai zurfi da walwalar ma’aikata, yana mai cewa matakan da aka dauka za su taimaka wajen rage basussukan ma’aikata da inganta ayyukan manyan makarantun jihar.














