Rundunar ’Yansandan Jihar Kebbi ta kama wani matashi mai shekaru 29, Abubakar Musa, bisa zargin haɗa baki da wasu mutane wajen wulaƙanta Alƙur’ani Mai Girma a Ƙaramar Hukumar Zuru.
Ana zargin Musa, wanda ke zaune a ƙauyen Rafin Mose da ke Zuru, da haɗa baki wajen aikata laifuka da suka haɗa da wulakanta Alƙur’ani, aikata tsafi da kuma ayyukan da ka iya haifar da tashin hankali a tsakanin al’umma.
A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau, ta ce lamarin ya faru ne ranar 9 ga watan Agusta, 2026, da misalin ƙarfe 7 na dare.
Rundunar ta ce bincike ya nuna cewa Musa ya haɗa baki da wasu mutane biyu, Rabi’u Tela, mijin Zarau Hassan, da Hamza Zango, inda suka tono wani rami a cikin ɗakin Zarau Hassan.
A cewar ’yansandan, an binne wani Alƙur’ani a cikin ramin tare da wasu abubuwa da suka haɗa da maniyyi, goro fari da ja, kayan cikin dabbobin da suka mutu da sauran abubuwan da ake zargin na tsafi ne.
Rundunar ta ce ana zargin an aikata hakan ne domin sanya Zarau Hassan ta zama mai biyayya ga mijinta, Rabi’u Tela.
Ta kuma ce irin wannan aiki na iya haifar da fitina da kawo cikas ga zaman lafiya tsakanin al’ummar Musulmi a yankin.
A halin yanzu, ’yansanda na neman Rabi’u Tela da Hamza Zango, waɗanda ake zargi da hannu a lamarin kuma duk sun tsere.
Rundunar ta ce Abubakar Musa yana hannun ’yansanda, kuma za a gurfanar da shi a gaban kotu bayan kammala bincike.
Kwamishinan ’Yansandan Jihar Kebbi, CP Umar M. Hadejia, ya yi Allah-wadai da lamarin.
Ya bayyana cewa rundunar za ta ɗauki matakin da ya dace bisa doka kan duk wanda ayyukansa za su kawo cikas ga zaman lafiya, tsaron jama’a da haɗin kan al’umma.














