Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Dr. Nasir Idris, ya sanar da sauyin mataimakin gwamna gabanin zaɓen gwamna na shekarar 2027. Ya Sauya Umar Abubakar Tafida Argungu daga matsayin abokin takararsa, sannan ya zabi Ibrahim Muhammad Augie a matsayin sabon mataimakin sa da za su yi takarar kujerar Gwamnan jihar a zaɓen 2027 mai zuwa.
Jam’iyyar APC ta bakin sakataren tsare-tsare na jam’iyyar a matakin kasa, Alhaji Suleiman Muhammad Argungu, ne ya sanar da hakan a madadin jam’iyyar a ranar Lahadi yayin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ɗakin gudanar da taro na masaukin shugaban kasa dake Birnin Kebbi.
“An sauya takarar mataimakin ne a matsayin abokin takarar Gwamna Nasir Idris Kauran Gwandu a zaɓen 2027 mai zuwa bisa shawarar da aka yanke a Jam’iyyance,” in ji Argungu.
Ya kara da cewa an dauki matakin ne da cikakken sani da yardar mataimakin gwamnan na yanzu wato Sanata Umar Abubakar Tafida Argungu. “Babu wani saɓani tsakanin Gwamna da mataimakinsa. An cimma wannan matsaya cikin lumana kuma don kare muradun jam’iyyar,” in ji shi.
Don haka, ya buƙaci ‘yan jam’iyyar APC, ‘yan siyasa, da magoya baya a faɗin jihar da su amince da wannan ci gaba tare da haɗa kai domin samun nasara a zaɓen 2027 mai zuwa.














