Fadar Shugaban Kasa ta ce masu sukar yadda gwamnatin tarayya ke tafiyar da batun rashin tsaro a Nijeriya suna yin watsi da irin sadaukarwa da nasarorin da sojojin kasar ke samu a kullum a fannoni daban-daban na ayyukan tsaro.
Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana hakan a cikin wata mukala mai taken “Murnar Jarumtar Ayyukan Sojojinmu a Fannonin Ayyuka Daban-daban”
Ya ce wasu ‘yan Nijeriya da “masu sharhi daga nesa” suna fi mayar da hankali kan munanan abubuwa kamar sace-sace, fashe-fashen abubuwan fashewa, hare-haren kunar bakin wake da sauran laifuka, yayin da suke yin watsi da nasarorin da sojoji ke samu.
A cewarsa, irin wannan fahimta na rage darajar jarumtar da jami’an rundunar sojin Nijeriya ke nunawa wajen yakar ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane, ‘yan bindiga da masu satar danyen mai.
Onanuga ya ce rahotannin tsaro na baya-bayan nan sun nuna cewa sojoji na samun gagarumar nasara a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda a sassa daban-daban na kasar.
Ya bayar da misali da ceto fasinjojin da aka yi garkuwa da su a Jihar Binuwe , inda sojojin Operation Whirl Stroke suka gudanar da aikin ceto cikin nasara a yankin Ohimini.
Haka kuma ya ambaci ayyuka a Jihar Filato, inda aka kama wadanda ake zargi da hannu a kashe-kashe, aka kwato makamai, tare da dakile satar shanu da kuma mayar da martani ga hare-hare.
A jihohin Borno da Yobe kuwa, ya ce sojoji sun kashe ‘yan ta’adda, sun dakile hare-hare, sannan sun kama masu safarar kayan taimakon ‘yan ta’adda da ake zargi suna da alaka da Boko Haram da ISWAP.
Ya kuma ce an gano tare da lalata abubuwan fashewa a wasu yankuna na Borno da Imo yayin sintiri da aikin share gari.
A Jihar Edo, sojoji sun dakile yunkurin garkuwa da mutane a Auchi, sun ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da kama wasu mutane. A jihar Kogi kuma, an lalata sansanin ‘yan ta’adda tare da kama wani mai kai musu kaya a wani aiki na hadin gwiwa.
Fadar Shugaban Kasa ta ce duk da kalubalen tsaro da ke ci gaba da wanzuwa, sojojin Nijeriya suna ci gaba da sadaukar da kansu wajen kare ‘yan kasa, inda wasu ke rasa rayukansu a bakin aiki.
Onanuga ya kara da cewa: “Kalubale na nan, kuma yakin bai kare ba. Amma abin da sojoji da gwamnati ke bukata daga mu shi ne godiya da karramawa, ba zagi da kushe ba.”















Discussion about this post