ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Sojojin Nijeriya Na Samun Nasarori Duk Da Kalubalen Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago

Fadar Shugaban Kasa ta ce masu sukar yadda gwamnatin tarayya ke tafiyar da batun rashin tsaro a Nijeriya suna yin watsi da irin sadaukarwa da nasarorin da sojojin kasar ke samu a kullum a fannoni daban-daban na ayyukan tsaro.

Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana hakan a cikin wata mukala mai taken “Murnar Jarumtar Ayyukan Sojojinmu a Fannonin Ayyuka Daban-daban”

Ya ce wasu ‘yan Nijeriya  da “masu sharhi daga nesa” suna fi mayar da hankali kan munanan abubuwa kamar sace-sace, fashe-fashen abubuwan fashewa, hare-haren kunar bakin wake da sauran laifuka, yayin da suke yin watsi da nasarorin da sojoji ke samu.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, irin wannan fahimta na rage darajar jarumtar da jami’an rundunar sojin Nijeriya  ke nunawa wajen yakar ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane, ‘yan bindiga da masu satar danyen mai.

Onanuga ya ce rahotannin tsaro na baya-bayan nan sun nuna cewa sojoji na samun gagarumar nasara a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda a sassa daban-daban na kasar.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

Ya bayar da misali da ceto fasinjojin da aka yi garkuwa da su a Jihar Binuwe , inda sojojin Operation Whirl Stroke suka gudanar da aikin ceto cikin nasara a yankin Ohimini.

Haka kuma ya ambaci ayyuka a Jihar Filato, inda aka kama wadanda ake zargi da hannu a kashe-kashe, aka kwato makamai, tare da dakile satar shanu da kuma mayar da martani ga hare-hare.

A jihohin Borno  da Yobe  kuwa, ya ce sojoji sun kashe ‘yan ta’adda, sun dakile hare-hare, sannan sun kama masu safarar kayan taimakon ‘yan ta’adda da ake zargi suna da alaka da Boko Haram da ISWAP.

Ya kuma ce an gano tare da lalata abubuwan fashewa a wasu yankuna na Borno da Imo yayin sintiri da aikin share gari.

A Jihar Edo, sojoji sun dakile yunkurin garkuwa da mutane a Auchi, sun ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da kama wasu mutane. A jihar Kogi kuma, an lalata sansanin ‘yan ta’adda tare da kama wani mai kai musu kaya a wani aiki na hadin gwiwa.

Fadar Shugaban Kasa ta ce duk da kalubalen tsaro da ke ci gaba da wanzuwa, sojojin Nijeriya suna ci gaba da sadaukar da kansu wajen kare ‘yan kasa, inda wasu ke rasa rayukansu a bakin aiki.

Onanuga ya kara da cewa: “Kalubale na nan, kuma yakin bai kare ba. Amma abin da sojoji da gwamnati ke bukata daga mu shi ne godiya da karramawa, ba zagi da kushe ba.”

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Next Post
Boko Haram Ta Kashe Manoma Da Masu Yankan Itace 20 A Wani Sabon Hari A Borno

Boko Haram Ta Kashe Manoma Da Masu Yankan Itace 20 A Wani Sabon Hari A Borno

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.