ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Sojojin Nijeriya Na Samun Nasarori Duk Da Kalubalen Tsaro

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

Fadar Shugaban Kasa ta ce masu sukar yadda gwamnatin tarayya ke tafiyar da batun rashin tsaro a Nijeriya suna yin watsi da irin sadaukarwa da nasarorin da sojojin kasar ke samu a kullum a fannoni daban-daban na ayyukan tsaro.

Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana hakan a cikin wata mukala mai taken “Murnar Jarumtar Ayyukan Sojojinmu a Fannonin Ayyuka Daban-daban”

Ya ce wasu ‘yan Nijeriya  da “masu sharhi daga nesa” suna fi mayar da hankali kan munanan abubuwa kamar sace-sace, fashe-fashen abubuwan fashewa, hare-haren kunar bakin wake da sauran laifuka, yayin da suke yin watsi da nasarorin da sojoji ke samu.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, irin wannan fahimta na rage darajar jarumtar da jami’an rundunar sojin Nijeriya  ke nunawa wajen yakar ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane, ‘yan bindiga da masu satar danyen mai.

Onanuga ya ce rahotannin tsaro na baya-bayan nan sun nuna cewa sojoji na samun gagarumar nasara a yakin da ake yi da ‘yan ta’adda a sassa daban-daban na kasar.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Ya bayar da misali da ceto fasinjojin da aka yi garkuwa da su a Jihar Binuwe , inda sojojin Operation Whirl Stroke suka gudanar da aikin ceto cikin nasara a yankin Ohimini.

Haka kuma ya ambaci ayyuka a Jihar Filato, inda aka kama wadanda ake zargi da hannu a kashe-kashe, aka kwato makamai, tare da dakile satar shanu da kuma mayar da martani ga hare-hare.

A jihohin Borno  da Yobe  kuwa, ya ce sojoji sun kashe ‘yan ta’adda, sun dakile hare-hare, sannan sun kama masu safarar kayan taimakon ‘yan ta’adda da ake zargi suna da alaka da Boko Haram da ISWAP.

Ya kuma ce an gano tare da lalata abubuwan fashewa a wasu yankuna na Borno da Imo yayin sintiri da aikin share gari.

A Jihar Edo, sojoji sun dakile yunkurin garkuwa da mutane a Auchi, sun ceto wadanda aka yi garkuwa da su tare da kama wasu mutane. A jihar Kogi kuma, an lalata sansanin ‘yan ta’adda tare da kama wani mai kai musu kaya a wani aiki na hadin gwiwa.

Fadar Shugaban Kasa ta ce duk da kalubalen tsaro da ke ci gaba da wanzuwa, sojojin Nijeriya suna ci gaba da sadaukar da kansu wajen kare ‘yan kasa, inda wasu ke rasa rayukansu a bakin aiki.

Onanuga ya kara da cewa: “Kalubale na nan, kuma yakin bai kare ba. Amma abin da sojoji da gwamnati ke bukata daga mu shi ne godiya da karramawa, ba zagi da kushe ba.”

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Boko Haram Ta Kashe Manoma Da Masu Yankan Itace 20 A Wani Sabon Hari A Borno

Boko Haram Ta Kashe Manoma Da Masu Yankan Itace 20 A Wani Sabon Hari A Borno

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.