Wasu daga cikin manoman Citta a Jihar Delta, sun soki gwamnatin jihar, kan rashin taimaka musu da kuma gazawar gwamnatin wajen cin gajiyar fannin.
Manoman, sun soki gwamnatin, kan rashin samar da cikakken ɗauki, musamman duba da bullar cutar da ke lalata Cittar da suka shuka.
A cewar manoman, a duk kakar noman Citta a jihar, suna tabka asara mai ɗimbin yawa tare da kuma rashin samun bashin da za su ci gaba da yin noma.
Kazalka, sun yi nuni da cewa; duk da irin ɗimbin albarkar da ke cikin noman nata, amma gwamnatin jihar ta mayar da manoman saniyar ware.
A cewar manoman, idan har ba a ɗauki matakan da suka dace ba, za a ci gaba da barin ƙasar a baya, musamman wajen ƙara habaka tattalin ƙasar.
“Muna buƙatar a mayar da hankali, domin bunƙasa fannin,” in ji shugaban ƙungiyar Chijioke Okafor.
“Rayuwarmu ta dogara ne kacokan, kan wannan fanni na noman Citta da fannin tattalin arziƙin ƙasar, wanda bai kamata a ce ƙasar ta gaza samun cin moriyar fannin ba,“ a cewarsa.
Shugaban ya kuma bayyana cewa, ta hanyar zuba jari a fannin, gwamnatin ƙasar za ta iya samun damar ƙara wadata ƙasar da abinci, musamman ta hanyar samarwa da manomanta kayan aiki na zamani.














Discussion about this post