Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi gargadin cewa matakin soji kadai ba zai iya kawo karshen rashin tsaro a yankin Arewa ta Tsakiya ba, yana mai kira ga al’ummomi, sarakunan gargajiya da shugabannin addini, matasa, mata da kuma ’yan kasuwa masu zaman kansu da su hada kai da hukumomin tsaro wajen yaki da miyagun laifuka tare da magance tushen matsalar tashin hankali.
Tinubu ya yi wannan kiran ne ranar Litinin a Taron Tsaro na Yankin Arewa ta Tsakiya na 2026 da aka gudanar a Makurdi, Jihar Benuwe, inda Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya wakilce shi.
Da yake magana kan taken taron, “Hanyoyin Hadin Gwiwa Wajen Karfafa Tsaro da Daidaiton Yanki,” Shugaban Kasar ya ce rashin tsaro ya zama mai sarkakiya sosai, wanda ya sa ba za a iya magance shi ta hanyar hukumar tsaro guda daya, gwamnati guda ko al’umma guda ba.
Ya ce, “Babu wata hukuma guda, babu wani matakin gwamnati guda, kuma babu wata al’umma guda da za ta iya tabbatar da tsaron wannan yanki ita kadai. Rashin tsaro ba ya mutunta iyakokin jihohi ko ikon hukumomi.”
Tinubu ya bukaci masu ruwa da tsaki su kawo karshen hamayya, maimaita ayyuka da kuma boye bayanan sirri, yana mai cewa miyagu kan rika tsallaka iyakokin kananan hukumomi da jihohi, yayin da martanin hukumomin tsaro ke kasancewa ba tare da cikakken hadin kai ba.
Yayin da yake yabawa rundunar soji, ’yansanda da hukumomin leken asiri kan nasarorin da suka samu a baya-bayan nan wajen yaki da ’yan ta’adda da sauran kungiyoyin masu aikata laifuka, ciki har da hallaka kwamandoji, mika wuya da mayakan suka yi da kuma ceto mutanen da aka yi garkuwa da su, Shugaban Kasar ya ce dole ne a hada ayyukan soji da matakan da za su magance abubuwan da ke haddasa tashin hankali.
Ya ce, “Matakin soji kadai ba zai samar da zaman lafiya mai dorewa a Arewa ta Tsakiya ba. Karfi na iya danne tashin hankali; amma ba zai warware korafe-korafen da ke haifar da shi ba.”
Tinubu ya bayyana rikicin neman filaye da ruwa, sauyin yanayi, yaduwar hamada, rikice-rikicen amfani da filaye da ba a warware su ba, raunin hanyoyin warware rikici a matakin al’umma da yaduwar makamai ba bisa ka’ida ba a matsayin wasu daga cikin abubuwan da ke ci gaba da haifar da rashin tsaro.
Ya bukaci sarakunan gargajiya da shugabannin addini su kasance sahun farko wajen kare al’umma daga barazanar da ke tasowa, ta hanyar bayar da gargadin farko da kuma inganta sulhu.
Ya ce, “Ina rokonku da ku kasance sahun farko wajen bayar da gargadin farko, kuma ku zama amintattun muryoyinmu wajen sasanta rikice-rikice.”
Ya kuma yi kira ga al’ummomi da su rika bai wa hukumomin tsaro bayanan sirri cikin lokaci tare da daina kare masu aikata laifuka saboda dangantakar iyali, kabila ko wasu alaka.
Ya ce, “Tsaro yana farawa ne daga gare ku. Ina kira ga kowane dan kasa da ya rika bai wa hukumomin tsaro bayanai, ya kuma daina kare aikata laifi saboda zumunci ko son rai.”
Shugaban Kasar ya ce mata da matasa dole su kasance a tsakiyar ayyukan samar da zaman lafiya, yayin da gwamnati za ta fadada hanyoyin samun guraben tattalin arziki domin rage sha’awar matasa shiga ayyukan laifi.














