Tsoma bakin kasashen waje a zaben Nijeriya ba sabon abu bane. Kafin zaben ranar 12 ga Yuni, an ji labarin cewa marigayi shugaban Libiyya, Muammar Gaddafi ya bayar da babban gudummawar kudi ga wasu ‘yan takara.
A shekarar 2015, tsohon shugaban kasa, Goodluck ya zargi John Kerry, wanda shi ne sakataren harkokin wajen Amurka a wancen lokaci, da yin wani shiri na kasashen yamma na kokarin raunana tazarcensa.
Haka kuma a shekarar 2023, Shugaban kasa, Bola Tinubu, wanda a wancan lokacin dan takara ne kawai, da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar sun yi kokarin samun neman goyon baya daga gwamnatin Joe Biden.
A shekarar 2027, shugabannin kasashen waje sun zuba idanu kan zaben Nijeriya, ciki har da Romauld Wadagni, Faure Gnassingbe, Omar Tchiani, Mohamed Bazoum, Assimi Goita, Ibrahim Traore, Mahamat Deby, har ma da kasashen yamma da ke fafatawa don samun tasiri a yammacin Afirka.
Dokar kasa ta dora wa hukumar leken asirin kasa (NIA) alhakin sa ido kan ayyukan wakilai da ma’aikatan kasashen waje.
Yayin da zaben ke karatowa, NIA da daraktanta, Mohammed Mohammed, na iya samun ayyuka da yawa da jerin kasashen da suke ganin suna da hannu a sakamakon zaben.
Moahemmed da kansa ba sabon abu bane a gareshi wajen yin aikin a kasashen da ke gudanar da kamfen din tasiri kan makwabtansu, kamar Koriya ta Arewa, Pakistan, da Libiya a karkashin shugabancin Gaddafi.
Amma yana fuskantar kalubale daban da na wadanda suka gabace shi, Yammacin Afirka ya sha bamban da matakin kashin kai da kuma kwarewa na aiki.
Uche Okeke ya yi kokari wajen kafa kwamitin leken asiri na harkokin tsaron Afirka. Olaniyi Oladeji ya shafe lokaci a Benin, shi kuma Ahmed Abubakar ya kwashe wani bangare na rayuwarsa a Chadi. Mohammed yana fuskantar yankin da aka karkasa.
A lokacin da tsohon shugaban rudunar sojojin Nijeriya, Tukur Bururai ya nuna yuwuwar katsalandar daga kasashen waje, babu wani shaida da ke nuna cewa makwabtan Nijeriya na kokarin yin tasiri a sakamakon zaben 2027.
Amma wasu suna matsayin abokan hulda na Rasha, kuma ba asirirce ba ne cewa wasu daga cikinsu suna da boyayyun fatan samun sauyi a siyasa.
Duk da haka, tsoma baki a zabe na iya bayyana ta hanyoyi kamar gudanar da kamfen a kafafen sada zumunta ta amfani da wakilan da aka biya, kutse cikin tsarin da ba shi da karfi, da kuma gina goyon baya ko adawa da ‘yan takara ta hanyar diflomasiyya.
A aikaice, Shugaba Tinubu ya kuma saka kansa cikin tsarin dimokuradiyya na kasashen makwabta kamar Nijar, Benin, Mali, da Burkina Faso.
A kasar Benin, Romuald Wadagni ba zai kasance shugaba a yau ba idan ba don Shugaba Tinubu ba. Duk da haka, tattalin arzikin kasa, kamar na Togo, ya sha tasiri ga manufofin gwamnatin Tinubu.
Masana’antar motoci ta Tokunbo a Benin, wacce take samun gagarumin tasiri daga Nijeriya, ta rushe. Hada kasuwar harkokin caji ya kuma sa kayayyaki da ayyuka sun yi arha a Nijeriya, wanda ya sa dole Benin ta rage abin da za ta fitar zuwa makwabciyarta.
Shugabannin kasashen Sahel na da korafe-korafe mafi girma fiye da tattalin arzikinsu. Rashin jin dadinsu ya juyawa zuwa zaman lafiyar siyasa da tsaro, kafuwar mulkin soja, da kuma kawo karshen tasirin mulkin mallaka.














